< Esajas 52 >

1 Vaagn op, vaagn op, ifør dig din Styrke, Zion! ifør dig din Herligheds Klæder, Jerusalem, du hellige Stad! thi ingen uomskaaren eller uren skal ydermere komme ind i dig.
Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
2 Ryst Støvet af dig, staa op, tag Sæde, Jerusalem! gør dig løs fra Lænkerne om din Hals, du Zions fangne Datter!
Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
3 Thi saa siger Herren: I ere solgte for intet, I skulle heller ikke løskøbes ved Penge.
Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
4 Thi saa siger den Herre, Herre: I Begyndelsen for mit Folk ned til Ægypten for at være fremmed der; og derpaa undertrykker Assur det for intet.
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
5 Og nu, hvad har jeg faaet her? siger Herren; thi mit Folk er bortført for intet; dets Herskere hyle, siger Herren, og mit Navn bespottes stedse den ganske Dag.
“Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
6 Derfor skal mit Folk lære at kende mit Navn; ja, derfor paa denne Dag; thi jeg er den, som taler, se, her er jeg.
Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
7 Hvor dejlige paa Bjergene ere dens Fødder, som bærer glædeligt Budskab, som forkynder Fred, som bærer glædeligt Budskab om godt, som forkynder Frelse og siger til Zion: Din Gud er Konge!
Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
8 Dine Vægteres Røst er der! de opløfte deres Røst, de synge alle med Fryd; thi med Øje imod Øje skue de, at Herren vender tilbage til Zion.
Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
9 Raaber med Fryd, synger med Jubel til Hobe, I Jerusalems øde Steder! thi Herren har trøstet sit Folk, han har genløst Jerusalem.
Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
10 Herren har blottet sin hellige Arm for alle Hedningernes Øjne, og alle Jordens Ender skulle se vor Guds Frelse.
Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
11 Bort, bort! drager ud derfra, rører ikke ved noget urent; gaar ud af dens Midte, renser eder, I, som bære Herrens Kar!
Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
12 Thi I skulle ikke drage ud med Hast ej heller gaa bort i Flugt; thi Herren gaar for eders Ansigt, og Israels Gud slutter eders Tog.
Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
13 Se, min Tjener skal handle klogelig; han skal ophøjes og opløftes og vorde saare høj.
Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
14 Ligesom mange forskrækkedes over ham — saa var hans Udseende skæmmet, at han ikke var som en Mand, og hans Skikkelse, at han ikke var som et Menneskens Barn, —
Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
15 saaledes skal han rense mange Hedninger, Konger skulle tillukke deres Mund for ham; thi hvad der ikke var fortalt dem, have de set, og hvad de ikke havde hørt, have de forfaret.
haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.

< Esajas 52 >