< Esajas 49 >

1 Hører mig, I Øer, og giver Agt, I Folk fra det fjerne! Herren kaldte mig fra Moders Liv af, han nævnede mit Navn fra Moders Skød.
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 Og han gjorde min Mund som et skarpt Sværd, skjulte mig med sin Haands Skygge, gjorde mig til en blank Pil og gemte mig i sit Kogger.
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 Og han sagde til mig: Du er min Tjener; du er Israel, i hvem jeg vil forherlige mig.
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 Men jeg sagde: Jeg har gjort mig Møje forgæves, fortæret min Kraft for intet og uden Nytte; alligevel er min Ret hos Herren og min Løn hos min Gud.
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 Og nu, siger Herren, som dannede mig af Moders Liv til sin Tjener, for at jeg skulde omvende Jakob til ham, og Israel, som ikke vil lade sig sanke; og jeg skal herliggøres for Herrens Øjne, og min Gud er min Styrke;
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 han siger: Det er for ringe en Ting, at du er min Tjener til at oprejse Jakobs Stammer og tilbageføre de bevarede af Israel, men jeg vil sætte dig til Hedningernes Lys, at de bringe min Frelse indtil Jordens Ende.
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 Saa siger Herren, Israels Genløser, hans Hellige, til den, som er foragtet af hver Sjæl, til den, som Folket har Afsky for, til Herskernes Tjener: Konger skulle se det og staa op, og Fyrster skulle se det og nedbøje sig for Herrens, Skyld, som er trofast, og for Israels Hellige, som udvalgte dig.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 Saa siger Herren: Paa den behagelige Tid bønhørte jeg dig, og paa Frelsens Dag hjalp jeg dig; og jeg vil bevare dig og sætte dig til en Pagt med Folket for at oprejse Landet og udskifte de øde Arvedele
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 for at sige til de bundne: Gaar ud! til dem, som ere i Mørke: Kommer frem for Lyset! de skulle finde Græsgang ved Vejene, og Græsgang skal være for dem paa alle nøgne Høje.
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 De skulle hverken hungre eller tørste, og ingen Hede eller Sol skal stikke dem; thi deres Forbarmer skal føre dem og lede dem til Vandkilder.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 Og jeg vil gøre alle mine Bjerge til Vej, og mine banede Veje skulle forhøjes.
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Se disse, de komme langt fra, og se disse, de komme fra Norden og fra Vesten, og disse, de komme fra Sinas Land.
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Synger med Fryd, I Himle! og fryd dig, du Jord! og I Bjerge, raaber med Frydesang! thi Herren trøster sit Folk og forbarmer sig over sine elendige.
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 Men Zion sagde: Herren har forladt mig, og Herren har glemt mig.
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 Kan vel en Kvinde glemme sit diende Barn, at hun ikke forbarmer sig over sit Livs Søn? om ogsaa de kunne glemme, da vil jeg, jeg dog ikke glemme dig.
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Se, jeg har tegnet dig i mine Hænder; dine Mure ere bestandig for mig.
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 Dine Børn komme i Hast; de, som nedbrøde og ødelagde dig, skulle drage ud fra dig.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Kast dine Øjne omkring og se, alle disse ere samlede, de komme til dig; saa sandt jeg lever, siger Herren, med alle disse skal du klæde dig som med en Prydelse, og du skal binde dem om dig, som Bruden sit Bælte.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 Ja, dine Ørkener og dine nedbrudte Stæder og det ødelagte Land, ja, det skal nu blive for snævert for Indbyggere, og de, som opslugte dig, skulle være langt borte.
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 End en Gang skulle dine Børn, som du maatte undvære, sige for dine Øren: Stedet er mig for trangt, giv mig Plads, at jeg maa bo der.
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 Og du skal sige i dit Hjerte: Hvo har avlet mig disse, eftersom jeg var barnløs og ufrugtbar? jeg var landflygtig og forskudt, og hvo har opdraget disse? se, jeg var enlig tilbage, hvor vare da disse?
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 Saa siger den Herre, Herre: Se, jeg vil udstrække min Haand efter Hedningerne og opløfte mit Banner for Folkene, og de skulle føre mine Sønner frem paa Armene, og dine Døtre skulle bæres paa Skuldrene.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 Og Konger skulle være dine Fosterfædre, og deres Fyrstinder skulle være dine Ammer, paa deres Ansigt skulle de nedbøje sig til Jorden for dig og slikke dine Fødders Støv: da skal du fornemme, at jeg er Herren, og at de, som forvente mig, ikke skulle beskæmmes.
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 Mon man kan tage fra den vældige, hvad han har taget? og mon den retfærdiges Fanger skulle undkomme?
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 Ja, saaledes siger Herren: Baade skulle Fangerne tages fra den vældige, og det, en Voldsmand har taget, skal rives fra ham; og jeg vil trætte med dem, som trætte med dig, og vil frelse dine Børn.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 Og jeg vil bringe dine Undertrykkere til at æde deres eget Kød, de skulle blive drukne af deres eget Blod som af Most; og alt Kød skal kende, at jeg, Herren, er din Frelser, og den Mægtige i Jakob er din Genløser.
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”

< Esajas 49 >