< Esajas 46 >

1 Bel synker i Knæ, Nebo synker sammen, deres Billeder lægger man paa Dyr og Fæ; hvad I bare, læsses som en Byrde paa de trætte Dyr.
Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
2 De synke sammen, de synke i Knæ til Hobe, de kunne ikke undkomme med Byrden; men de selv maa gaa i Fangenskab.
Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
3 Hører mig, Jakobs Hus og alle I overblevne af Israels Hus, I, som ere lagte paa mig fra Moders Liv af, I, som bæres af mig fra Moders Skød af!
“Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
4 Ja, indtil eders Alderdom skal jeg være den samme og bære eder indtil eders graa Haar; jeg har gjort det og skal fremdeles holde eder oppe, og jeg vil bære eder og lade eder undkomme.
Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
5 Ved hvem ville I ligne mig, eller med hvem ville I stille mig sammen? og hvem ville I maale mig med, at vi skulle være hverandre lige?
“Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
6 De ryste Guld ud af Pungen og veje Sølv paa Vægten, de lønne en Guldsmed, at han skal gøre en Gud deraf, for hvilken de falde paa Knæ og nedbøje sig.
Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
7 De løfte den op, de bære den paa Skuldrene og sætte den paa dens Sted; der staar den, den viger ikke fra sit Sted, vil nogen end raabe til den, skal den dog ikke svare, den kan ikke frelse nogen af hans Nød.
Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
8 Kommer dette i Hu og værer mandige; I Overtrædere! lægger det paa Hjerte!
“Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
9 Kommer de forrige Ting fra gammel Tid i Hu; thi jeg er Gud og ingen ydermere, ja, jeg er Gud, og ingen er som jeg,
Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
10 jeg, som fra Begyndelsen kundgør Enden og fra fordums Tid de Ting, som end ikke ere skete; jeg, som siger: Mit Raad skal bestaa, og jeg vil gøre alt det, som mig behager;
Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
11 jeg, som kalder en Rovfugl fra Østen, en Mand, som skal gøre efter mit Raad, fra et langt fraliggende Land; jeg har baade talt det og vil lade det komme, og jeg har beskikket det, jeg vil ogsaa udføre det.
Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
12 Hører mig, I, som ere stolte i Hjertet! I, som ere langt fra Retfærdighed!
Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
13 Jeg har ladet min Retfærdighed komme nær til, den er ikke langt borte, og min Frelse tøver ikke; jeg vil give Frelse i Zion og min Herlighed over Israel.
Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.

< Esajas 46 >