< Esajas 37 >

1 Og det skete, der Kong Ezekias hørte det, da sønderrev han sine Klæder og iførte sig Sæk og gik ind i Herrens Hus.
Sa’ad da Sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakkece rigunansa ya kuma sanya tsummoki ya tafi ya shiga haikalin Ubangiji.
2 Og han sendte Eliakim, som var Hofmester, og Sebna, Kansleren, og de ældste af Præsterne, som havde iført sig Sæk, til Profeten Esajas, Amoz's Søn.
Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna magatakarda da kuma manyan firistoci, duka sanye da tsummoki, wurin Ishaya ɗan Amoz.
3 Og de sagde til ham: Saa sagde Ezekias: Denne Dag er Nødens og Tugtelsens og Bespottelsens Dag; thi Børnene ere komne til Fødselens Sted, og der er ingen Kraft til at føde.
Suka faɗa masa cewa, “Ga abin da Hezekiya ya ce wannan rana ce ta baƙin ciki da tsawatawa da shan kunya, sai ka ce sa’ad da’ya’ya kan zo matakin haihuwa sa’an nan a rasa ƙarfin haihuwarsu.
4 Maaske Herren din Gud vil høre Rabsakes Ord, hvem hans Herre, Kongen af Assyrien, sendte for at forhaane den levende Gud, og han vil straffe ham for de Ord, som Herren din Gud har hørt; saa opløft en Bøn for de overblevne, som findes.
Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka zai ji maganganun sarkin yaƙin da maigidansa, sarkin Assuriya, ya aika don yă zagi Allah mai rai, ya kuma tsawata masa saboda maganganun da Ubangiji Allahnka ya ji. Saboda haka ka yi addu’a saboda raguwar da suke da rai.”
5 Der Kong Ezekias's Tjenere kom til Esajas,
Sa’ad da shugabannin Sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,
6 da sagde Esajas til dem: Saa skulle I sige til eders Herre: Saa sagde Herren: Frygt ikke for de Ord, som du hørte, dem, hvormed Kongen af Assyriens Tjenere forhaanede mig.
sai Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku cewa, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa. Kada ka ji tsoron abin da ka ji, maganganun nan da bayin sarkin Assuriya suka yi mini saɓo.
7 Se, jeg vil indgive ham en Aand, og han skal høre et Rygte og drage tilbage til sit Land, og jeg vil fælde ham med Sværd i hans Land.
Ka saurara! Zan sa ruhuna a cikinsa saboda sa’ad da ya ji wani labari, zai koma zuwa ƙasarsa, a can kuwa zan sa a kashe shi da takobi.’”
8 Og der Rabsake kom tilbage, da, fandt han, at Kongen af Assyrien stred imod Libna; thi han hørte, at han var rejst fra Lakis.
Sa’ad da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye ya kuma sami sarki yana yaƙi da Libna.
9 Og der han hørte om Thiraka, Morlands Konge, og der sagdes: Han er dragen ud at stride imod dig: — Der han hørte det, da sendte han Bud til Ezekias og lod sige:
To, fa, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana fitowa don yă yi yaƙi da shi. Sa’ad da ya ji haka, sai ya aiki jakadu zuwa wurin Hezekiya da wannan magana.
10 Saa skulle I sige til Ezekias, Judas Konge: Lad din Gud, som du forlader dig paa, ikke bedrage dig, saa at du siger: Jerusalem skal ikke gives i Kongen af Assyriens Haand.
“Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda cewa kada ka bar allahn da ka dogara a kai ya ruɗe ka sa’ad da ya ce, ‘Ba za a ba da Urushalima ga sarkin Assuriya ba.’
11 Se, du har hørt, hvad Kongerne af Assyrien have gjort ved alle Landene, at de have ødelagt dem, og skulde du blive friet?
Tabbatacce ka ji abin da sarakunan Assuriya suka aikata ga dukan ƙasashe, suna hallaka su tas. Kai kuwa za ka tsira ne?
12 Have Hedningernes Guder friet dem, som mine Fædre ødelagde, nemlig Gosan og Haran og Rezef og Edens Børn, som vare i Telassar?
Allolin al’umman da kakannina suka hallaka sun cece su ne, allolin Gozan, Haran, Rezef da kuma na mutanen Eden waɗanda suke zama a Tel Assar?
13 Hvor er Kongen af Hamat og Kongen af Arfad og Kongen af Sefarvajms Stad og af Hena og Jova?
Ina sarkin Hamat yake, sarkin Arfad fa, sarkin Sefarfayim, ko na Hena ko na Iffa?”
14 Og Ezekias tog Brevene af Budenes Haand og læste dem; og han gik op til Herrens Hus, og Ezekias udbredte dem for Herrens Ansigt.
Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga jakadun ya karanta ta. Sa’an nan ya haura zuwa haikalin Ubangiji ya shimfiɗa ta a gaban Ubangiji.
15 Og Ezekias bad til Herren og sagde:
Sai Hezekiya ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
16 Herre Zebaoth, Israels Gud! du, som sidder over Keruber, du alene er Gud over alle Riger paa Jorden, du gjorde Himlene og Jorden.
“Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, zaune a tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah a kan dukan masarautan duniya.
17 Herre! bøj dit Øre og hør; Herre! oplad dine Øjne og se; og hør alle, Senakeribs Ord, som han sendte for at haane den levende Gud.
Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka kuma ji; ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka kuma gani; ka saurara ga dukan maganganun da Sennakerib ya aika don yă zagi Allah mai rai.
18 Det er sandt, Herre! Kongerne af Assyrien have ødelagt alle Landene og deres eget Land.
“Gaskiya ce, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriyawa sun mai da dukan waɗannan mutane da ƙasashensu kango.
19 Og de have overgivet deres Guder til Ilden, fordi de ikke vare Guder, men Menneskenes Hænders Gerning, Træ og Sten, og de tilintetgjorde dem.
Sun jefar da gumakansu cikin wuta suka kuma hallaka su, gama su ba alloli ba ne itace ne kawai da dutse, da hannuwan mutane suka sarrafa.
20 Men nu, Herre vor Gud! frels os fra hans Haand, at alle Riger paa Jorden maa kende, at du er Herre, du alene.
Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, saboda masarautai a duniya su san cewa kai kaɗai ne, ya Ubangiji, Allah.”
21 Da sendte Esajas, Amoz's Søn, til Ezekias og lod sige: Saa giger Herren, Israels Gud: Du har bønfaldet mig angaaende Senakerib, Kongen af Assyrien.
Sa’an nan Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wa Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa. Saboda ka yi addu’a gare ni game da Sennakerib sarkin Assuriya,
22 Dette er det Ord, som Herren har talt imod ham: Jomfruen, Zions Datter, foragter dig og spotter dig, Jerusalems Datter ryster med Hovedet ad dig.
ga abin da maganar Ubangiji ya faɗa a kansa, “Budurwa Diyar Sihiyona ta rena tana kuma maka ba’a. Diyar Urushalima tana kada kai yayinda kake gudu.
23 Hvem har du bespottet og forhaanet? og imod hvem opløftede du Røsten? og du opløftede dine Øjne højt imod Israels Hellige.
Wane ne ka zargi ka kuma yi wa saɓo? A kan wa ka tā da muryarka ka kuma daga idanu cikin fariya? A kan Mai Tsarkin nan na Isra’ila!
24 Du bespottede Herren ved dine Tjenere og sagde: Med mine Vognes Mangfoldighed er jeg opfaren paa Bjergenes Højder, Libanons Toppe; og jeg vil afhugge dens høje Cedre, dens udvalgte Fyrre, og jeg vil komme til dens højeste Tinde, til dens frodige Skov.
Ta wurin jakadunka ka jibge zage-zage a kan Ubangiji. Ka kuma ce, ‘Da kekunan yaƙina masu yawa na hau ƙwanƙolin duwatsu, ƙwanƙolin mafi tsayi na Lebanon. Na sassare al’ul mafi tsayi fir mafi kyau. Na kai can wuri mafi nisa na kurminsa.
25 Jeg har gravet Brønde og drukket Vand og udtørret alle dybe Floder med mine Fødders Saaler.
Na haƙa rijiyoyi a baƙuwar ƙasa na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.’
26 Har du ikke hørt, at jeg har gjort dette for lang Tid siden, at jeg har beskikket det i gamle Dage? nu har jeg ladet det komme, og det skal være til at ødelægge de faste Stæder, at de blive til øde Grushobe.
“Ba ka ji ba cewa tun dā can na shirya ya zama haka? A kwanakin dā na kafa shi; yanzu na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu mafaka zuwa tsibin ɓuraguzai.
27 Og de, som bo deri, bleve afmægtige, bleve knuste og beskæmmede; de bleve som Græs paa Marken og som de grønne Urter, som Hø paa Tagene og som Korn, der er blevet forbrændt, før, det sætter Aks.
Mutanensu, suka rasa ƙarfi, sun firgita suka kuma sha kunya. Suka zama kamar tsire-tsire a gona, kamar tsire-tsiren ta suka tohu, kamar ciyawar da ya tsiro a kan rufi, wadda zafi ya yi wa ƙuna kafin tă yi girma.
28 Og jeg ved din Bolig og din Udgang og din Indgang, og at du raser imod mig.
“Amma na san inda kake zama da sa’ad da kakan fita ka kuma koma da yadda ka harzuƙa gāba da ni.
29 Efterdi du raser imod mig, og din Sorgløshed er kommen op for mine Øren, saa vil jeg lægge min Krog i din Næse og mit Bidsel i dine Læber og føre dig tilbage ad den Vej, som du kom paa.
Saboda ka harzuƙa gāba da ni kuma saboda girmankanka ya kai kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma ta hanyar da ka zo.
30 Og dette skal være dig Tegnet: At man i dette Aar skal æde det, som opvokser uden Arbejde, og i det andet Aar det, som vokser af sig selv; men i det tredje Aar saar da og høster, og planter Vingaarde og æder deres Frugt!
“Wannan zai zama alama gare ka, ya Hezekiya, “Wannan shekara za ka ci abin da ya yi girma da kansa, shekara ta biyu kuma abin da ya tsiro daga wancan. Amma a shekara ta uku za ka yi shuki ka kuma girba, za ka dasa gonakin inabi ka kuma ci’ya’yansu.
31 Thi det undkomne, som er overblevet af Judas Hus, skal atter faa Rødder nedefter og bære Frugt opefter.
Sauran da suka rage na gidan Yahuda kuwa za su yi saiwa a ƙarƙashi su kuma ba da’ya’ya a bisa.
32 Thi fra Jerusalem skal der udgaa nogle overblevne og fra Zions Bjerg nogle undkomne; den Herre Zebaoths Nidkærhed skal gøre det.
Gama daga Urushalima raguwa za tă fito, kuma daga Dutsen Sihiyona ƙungiyar waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki zai cika wannan.
33 Derfor saa siger Herren om Kongen af Assyrien: Han skal ikke komme ind i denne Stad og ikke skyde en Pil derind og ikke komme for den med Skjold og ingen Vold opkaste imod den.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga wannan birni ba ya harbe kibiya a nan. Ba zai zo gabansa da garkuwa ba ko ya gina mahaurai kewaye a kansa ba.
34 Han skal drage tilhage ad den Vej, som han kom paa, og ikke komme ind i denne Stad, siger Herren.
Ta hanyar da ya zo da ita zai koma; ba zai shiga wannan birni ba,” in ji Ubangiji.
35 Men jeg vil beskærme denne Stad for at frelse den, for min Skyld og for Davids, min Tjeners, Skyld.
“Zan kāre wannan birni in kuma cece shi, saboda girmana da kuma saboda sunan Dawuda bawana!”
36 Da for Herrens Engel ud og slog i Assyrernes Lejr hundrede og fem og firsindstyve Tusinde; og der man stod aarle op om Morgenen, se, da vare de alle sammen døde Kroppe.
Sai mala’ikan Ubangiji ya fita ya kuma karkashe mutane dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar a sansanin Assuriya. Sa’ad da mutane suka farka kashegari, sai ga gawawwaki duk a kwance!
37 Saa rejste Senakerib, Kongen af Assyrien, og drog bort og vendte tilbage, og han blev i Ninive.
Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya janye. Ya koma zuwa Ninebe ya zauna a can.
38 Og det skete, der han tilbad i Nisroks, sin Guds, Hus, da ihjelsloge hans Sønner, Adramelek og Sar-Ezer, ham med Sværd, og de undkom til Ararats Land, og hans Søn Asarhaddon blev Konge i hans Sted.
Wata rana, yayinda yake yin sujada a haikalin allahnsa Nisrok,’ya’yansa maza Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka kuma gudu zuwa ƙasar Ararat. Esar-Haddon ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.

< Esajas 37 >