< Esajas 32 >
1 Se, med Retfærdighed skal en Konge regere, og efter Ret skulle Fyrsterne styre.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 Og enhver af dem skal være som Skjul imod Vejr og Ly imod Vandskyl, som Vandbække paa et tørt Sted og som en svar Klippes Skygge i et vansmægtende Land.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 Og de seendes Øjne skulle ikke være blændede, og de hørendes Øren skulle give Agt.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 Og de ubesindiges Hjerte skal forstaa Kundskab; og de stammendes Tunge skal haste til at tale forstaaelige Ord.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 En Daare skal ikke ydermere kaldes ædel og en karrig ej kaldes rig.
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 Thi en Daare taler Daarlighed, og hans Hjerte gør Uret for at øve Ugudelighed og for at tale Usandhed imod Herren, for at lade en hungrig Sjæl forblive tom og lade en tørstig fattes Drik.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 Og den karrige bruger slette Midler; han optænker List for at berede de elendige Fordærvelse med falske Ord, og det, naar den fattige taler sin Sag.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 Men den ædle tænker paa ædle Ting, han skal bestaa ved sin ædle Daad.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 I Kvinder, som ere saa sorgløse, staar op og hører min Røst! I Døtre, som ere saa trygge, vender Øren til min Tale!
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 Om Aar og Dag skulle I, som ere trygge, blive urolige; thi det er forbi med Vinhøsten, der kommer ingen Frugtsamling.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 Vorder forfærdede, I sorgløse! vorder urolige, I trygge! klæd dig af, og blot dig, og bind om Lænderne!
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 De skulle slaa sig for Brystet for de yndige Agres, for de frugtbare Vintræers Skyld;
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 der skal opvokse Torne og Tidsler paa mit Folks Mark, ja, over alle Glædens Boliger i den lystige Stad.
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 Thi Paladserne ere forladte, Stadens Tummel er ophørt; Ofel og Vagttaarnet er blevet til Huler evindelig, Vildæsler til Glæde, Hjorde til Føde,
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 indtil Aanden fra det høje udgydes over os, og Ørken bliver til en frugtbar Mark, og den frugtbare Mark agtes som en Skov;
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 og Ret bor i Ørken, og Retfærdighed bliver paa den frugtbare Mark;
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 og Retfærdigheds Gerning bliver Fred, og Retfærdighedens Løn bliver Hvile og Tryghed indtil evig Tid;
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 og mit Folk bor i Fredens Hytter og i Trygheds Boliger og i stille rolige Steder.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 Men det skal hagle, naar Skoven fældes, og Staden skal nedtrykkes i det lave.
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Lyksalige ere I, som saa ved alle Vande, I, som lade Oksen og Æselet frit løbe om!
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.