< Esajas 31 >

1 Ve dem, som fare ned til Ægypten om Hjælp og forlade sig paa Heste og sætte Tillid til Vogne, fordi disse ere mange, og til Ryttere, fordi disse ere saare stærke, men se ikke hen til den Hellige i Israel og søge ikke Herren!
Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
2 Men ogsaa han er viis og lader Ulykke komme og tager ikke sine Ord tilbage, men han rejser sig imod de ondes Hus og imod deres Hjælpere, som gøre Uret.
Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
3 Thi Ægypterne ere Mennesker og ikke Gud, og deres Heste ere Kød og ikke Aand; og Herren skal udstrække sin Haand, at Hjælperen skal støde sig, og den, som bliver hjulpen, skal falde, at de alle skulle omkomme til Hobe.
Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
4 Thi saa sagde Herren til mig: Ligesom en Løve og en ung Løve brøler over sit Rov, og som den, skønt mangfoldige Hyrder kaldes imod den, ikke forskrækkes for deres Skrig og ikke bliver bange for deres Støj: Saa skal den Herre Zebaoth nedfare at stride paa Zions Bjerg og paa dens Høj.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
5 Som flyvende Fugle, saa skal den Herre Zebaoth beskærme Jerusalem; han skal beskærme og frelse, han skal gaa forbi og redde.
Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
6 Vender om til ham, som Israels Børn ere dybt affaldne fra!
Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
7 Thi paa den Dag skal enhver forkaste sine Sølvafguder og sine Guldafguder, hvilke eders Hænder gjorde eder til Synd.
Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
8 Og Assur skal ikke falde ved Mands Sværd, men et Sværd, som ikke er et Menneskes, skal fortære ham; og han skal fly for Sværdet, og hans unge Karle skulle gøres til Trælle;
“Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
9 Og sin Klippe skal han gaa forbi af Frygt, og hans Fyrster skulle forskrækkes for Banneret, siger Herren, som har sin Ild i Zion og sin Ovn i Jerusalem.
Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.

< Esajas 31 >