< Esajas 26 >
1 Paa den Dag skal denne Sang synges i Judas Land: Vi have en stærk Stad, Frelse sætter han til Mure og Værn.
A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
2 Oplader Portene, at der maa indgaa et retfærdigt Folk, som bevarer Troskab.
A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
3 Den Fortrøstning staar fast: Du bevarer Fred, Fred; thi paa dig forlader man sig.
Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
4 Forlader eder paa Herren stedse og altid; thi den Herre, Herre er en evig Klippe.
Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
5 Thi han nedbøjer dem, som bo i det høje, den ophøjede Stad; han skal fornedre den, han skal fornedre den til Jorden, han skal slaa den ned indtil Støvet.
Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
6 Foden skal nedtræde den, den elendiges Fødder, de ringes Fodtrin.
Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
7 Den retfærdiges Sti er jævn; du jævner den retfærdiges Vej.
Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
8 Ja, paa dine Dommes Sti, Herre! have vi forventet dig; til dit Navn og til din Ihukommelse er vor Sjæls Længsel.
I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
9 Med min Sjæl længes jeg efter dig om Natten; med min Aand i mit Indre vil jeg søge dig aarle; thi naar dine Domme komme ned til Jorden, da lære Jorderiges Indbyggere Retfærdighed.
Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
10 Bliver den ugudelige benaadet, da lærer han ikke Retfærdighed; han gør Uret i Rettens Land og ser ikke Herrens Højhed.
Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
11 Herre! din Haand er høj, dog skue de det ikke; de skulle skue din Nidkærhed for dit Folk og beskæmmes; ja, Ilden skal fortære dem, som ere dine Fjender.
Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
12 Herre! du skal skaffe os Fred; thi endog alle vore Gerninger har du gjort for os.
Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
13 Herre, vor Gud! der have andre Herskere hersket over os foruden dig; ved dig alene prise vi dit Navn.
Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
14 De døde leve ikke op igen, Dødningerne opstaa ikke; derfor har du hjemsøgt og ødelagt dem og udslettet al deres Ihukommelse.
Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
15 Du formerede Folket, Herre! du formerede Folket, du er bleven herliggjort; du har flyttet alle Landets Grænser langt bort.
Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
16 Herre! i Angesten søgte de dig, de udøste deres stille Bøn, der du tugtede dem.
Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
17 Ligesom den frugtsommelige, naar hun er nær ved at føde, bliver bange og raaber i sine Veer, saa gik det os, Herre! for dit Ansigt.
Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
18 Vi gik frugtsommelige med noget, vare bange, men da vi fødte, blev det til Vind; vi skaffede Landet ikke nogen Frelse, og Jorderiges Indbyggere kom ej til Live.
Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
19 Dine døde skulle leve, mine afdøde skulle opstaa; vaagner op, og synger med Fryd, I som bo i Støv! thi din Dug er Dug over grønne Urter, og Jorden skal give Dødningerne tilbage.
Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
20 Gak, mit Folk! gak ind i dine inderste Kamre, og luk dine Døre efter dig; skjul dig et lidet Øjeblik, indtil Vreden gaar over.
Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
21 Thi se, Herren gaar ud fra sit Sted for at hjemsøge Jordens Indbyggeres Misgerning; og Jorden skal aabenbare det udgydte Blod og ikke længere skjule sine ihjelslagne.
Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.