< Esajas 25 >
1 Herre! du er min Gud, jeg vil ophøje dig, jeg vil bekende dit Navn; thi du gjorde Under; de Raad, som ere fattede længe tilforn, ere Trofasthed og Sandhed.
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
2 Thi du gjorde af Staden en Stenhob, af den faste Stad en Grushob, de fremmedes Paladser ere ikke længer en Stad; den skal ikke bygges evindelig.
Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
3 Derfor skal et mægtigt Folk ære dig; grumme Hedningers Stæder skulle frygte dig.
Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
4 Thi du var den ringes Styrke, den fattiges Styrke, da han var i Angest, en Tilflugt imod Regnskyl, en Skygge imod Heden; thi de grummes Fnysen er som Regnskyl imod en Væg.
Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
5 Som Heden i det tørre Land, saa nedtrykker du de fremmedes Bulder; som Heden ved Skyggen af en Sky, saa dæmpes de grummes Sang.
kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
6 Og den Herre Zebaoth skal gøre for alle Folkeslag et fedt Gæstebud paa dette Bjerg, et Gæstebud med gammel Vin, med fed Marv, med gammel, klaret Vin.
A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
7 Og paa dette Bjerg skal han borttage Sløret, med hvilket alle Folkeslag ere tilslørede, og Dækket, hvormed alle Hedninger ere bedækkede.
A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
8 Han skal opsluge Døden for evig, og den Herre, Herre skal afviske Graaden af alle Ansigter og borttage sit Folks Forsmædelse af al Jorden; thi Herren har talt det.
zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
9 Og man skal sige paa den Dag: Se, dette er vor Gud, vi have haabet paa ham, og han skal frelse os; dette er Herren, vi have haabet paa ham, vi ville fryde og glæde os ved hans Frelse.
A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
10 Thi Herrens Haand skal hvile over dette Bjerg; men Moab skal nedtrædes, som man nedtræder Halm i Møddingpølen.
Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
11 Og det skal brede sine Hænder ud deri, ligesom den, der svømmer, udbreder dem for at svømme; og han skal nedtrykke dets Hovmod tillige med dets Hænders Ranker.
Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
12 Og dine høje Mures Befæstning skal han styrte, nedkaste, slaa til Jorden indtil Støvet.
Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.