< Esajas 22 >
1 Profeti imod Synernes Dal. Hvad fattes dig dog, at du med alle dine saaledes stiger op paa Tagene?
Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
2 Du, som var fuld af Brusen, du støjende Stad, du jublende By! dine ihjelslagne ere ikke ihjelslagne med Sværd og ikke døde i Krigen.
Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
3 Alle dine Fyrster ere flygtede til Hobe, tiden Bue ere de fangne; alle; som fandtes i dig, ere fangne, til Hobe, de maatte fly langt bort.
Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
4 Derfor siger jeg: Ser bort fra mig, jeg vil beskelig græde; trænger ikke paa for at trøste mig over mit Folks Datters Ødelæggelse.
Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
5 Thi der er en Forstyrrelses og Nedtrædelses og Forvirrings Dag fra Herren, den Herre Zebaoth, i Synernes Dal, paa Hvilken Murene blive nedbrudte, og man raaber imod Bjergene.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
6 Og Elam bar Kogger, fulgt af Vogne med Mænd paa og af Ryttere, og Kir blottede Skjoldet.
Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
7 Og det skete, at dine udvalgte Dale bleve fulde af Vogne, og Ryttere toge Stilling imod Porten.
Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
8 Og han borttog Dækket fra Juda; og du saa dig om paa den Dag efter Rustningen i Skovhuset.
An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
9 Og I saa Revnerne paa Davids Stad, at de vare mange, og I samlede den nederste Dams Vand.
kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
10 Og I talte Jerusalems-Huse og nedbrøde Huse for at befæste Muren.
Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
11 Og I gjorde en Grav imellem de tvende Mure for Vandet af den gamle Dam; men I saa ikke hen til ham, som havde beskikket det, til ham, som havde besluttet det for lang Tid siden, saa I ikke.
Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
12 Og Herren, den Herre Zebaoth, opfordrede paa den Dag til Graad og Sorg og til at gøre Hovedet skaldet og til at ombinde sig med Sæk.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
13 Men se, der er Fryd og Glæde, man ihjelslaar Øksne og slagter Faar, æder Kød og drikker Vin: „Lader os æde og drikke; thi vi skulle dø i Morgen!”
Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
14 Men den Herre Zebaoth har saaledes aabenbaret sig for mine Øren: Denne Misgerning skal ikke udsones for eder, inden I dø! siger Herren, den Herre Zebaoth.
Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
15 Saa sagde Herren, den Herre Zebaoth: Gak, kom ind til denne Rentemester, til Sebna, som er Hofmester, og sig til ham:
Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
16 Hvad har du her? og hvem har du her, at du har hugget dig her en Grav? som den, der lader hugge sin Grav i det høje, som den, der lader sig en Bolig udhule i Klippen!
Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
17 Se, Herren skal bortkaste dig med et Kast, du Mand! og skjule dig aldeles.
“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
18 Han skal sno dig sammen i en Snoning, som en Bold, hen til et vidt og bredt Land; der skal du dø, og der skulle dine herlige Vogne komme hen, du, som er en Skændsel for din Herres Hus!
Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
19 Og jeg vil støde dig ned fra dit Stade, og han skal nedkaste dig fra din Plads,
Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
20 Og det skal ske paa den Dag, da vil jeg kalde ad min Tjener Eliakim, Hilkias Søn.
“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
21 Og jeg vil iføre ham din Kjortel og styrke ham med dit Bælte og give dit Herredømme i hans Haand; og han skal være en Fader for dem, som bo i Jerusalem, og for Judas Hus.
Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
22 Og jeg vil lægge Nøglen til Davids Hus paa hans Skuldre, og han skal oplade, og ingen skal tillukke, og han skal tillukke, og ingen skal oplade.
Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
23 Og jeg vil fæste ham som en Nagle paa et fast Sted, og han skal være et Ærens Sæde for sin Faders Hus.
Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
24 Og de skulle hænge paa ham al hans Faders Hus's Herlighed, de ædle og de vilde Skud, alle Smaakar, baade Bægere og alle Flasker.
Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
25 Paa den Dag, siger den Herre Zebaoth, skal Naglen borttages, den, som var fæstet paa et fast Sted, og den skal afhugges og falde, og den Byrde, som hang derpaa, skal ødelægges; thi Herren har talt det.
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.