< Esajas 19 >

1 Profeti imod Ægypten. Se, Herren farer paa en let Sky og kommer til Ægypten, og Ægyptens Afguder skulle bæve for hans Ansigt og Ægypternes Hjerte blive modfaldent i deres Inderste.
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
2 Og jeg vil væbne Ægypter imod Ægypter, og de skulle stride hver imod sin Broder og hver imod sin Næste, Stad imod Stad, Rige imod Rige.
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
3 Og Ægypternes Aand i deres Indre skal udtømmes, og jeg vil tilintetgøre deres Raad, saa de skulle adspørge hos Afguderne og hos Troldkarlene og hos Spaakvinderne og hos Tegnsudlæggerne.
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
4 Og jeg vil overantvorde Ægypterne i en haard Herres Haand, og en streng Konge skal herske over dem, siger Herren, den Herre Zebaoth.
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
5 Og Vandet skal svinde af Søen, og Floden skal udtørres og blive tør.
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
6 Og Floderne skulle stinke, de dybe Strømme skulle formindskes og blive tørre, Rør og Tang skal visne hen.
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
7 Engene ved Nilen, ved Bredden af Nilen, og al Sæd ved Nilen skal borttørres, henvejres og ikke være mere til.
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
8 Og Fiskerne skulle blive bedrøvede, og alle, som kaste Krog i Nilen, skulle sørge, og de, som sætte Garn ud paa Vandet, skulle vansmægte.
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
9 Og beskæmmes skulle de, som arbejde i Hør, og de, som væve hvidt Tøj.
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
10 Og deres Grundpiller skulle ligge knuste, alle de, som arbejde for Løn, skulle være bedrøvede i Sjælen.
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
11 Fyrsterne i Zoan ere kun Daarer, Faraos vise Raadgiveres Raad er blevet ufornuftigt; hvorledes kunne I sige til Farao: Jeg er de vises Søn, Fortids Kongers Søn?
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
12 Hvo ere de dog, disse dine vise? Lad dem kundgøre dig, og lad dem selv erkende, hvad den Herre Zebaoth har raadslaget over Ægypten!
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
13 Fyrsterne i Zoan ere blevne til Daarer, Fyrsterne i Nof ere bedragne, og Stammernes Overhoveder have forvildet Ægypten.
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
14 Herren har ladet komme en Forvirrings Aand iblandt dem, og den har forvildet Ægypten i al dets Gerning, ligesom en drukken er forvildet, naar han spyr.
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
15 Og for Ægypten skal intet lykkes, som Hoved eller Hale, Palmegren eller Siv skal faa gjort.
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
16 Paa denne Dag skulle Ægypterne være som Kvinder og forfærdes og frygte for den Herre Zebaoths opløftede Haand, hvilken han skal opløfte over dem.
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
17 Og Judas Land skal være Ægypterne til Forfærdelse; naar nogen minder dem derom, skulle de frygte for den Herre Zebaoths Raad, som han har raadslaget over dem.
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
18 Paa denne Dag skal der være fem Stæder i Ægyptens Land, som skulle tale med Kanaans Tungemaal og sværge til den Herre Zebaoth; en af dem skal kaldes Ir-Haheres.
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
19 Paa denne Dag skal der være et Alter for Herren midt i Ægyptens Land og en Mindestøtte for Herren ved dets Grænse.
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
20 Og det skal være for den Herre Zebaoth til et Tegn og til et Vidnesbyrd i Ægyptens Land, at naar de raabe til Herren for deres Skyld, som fortrykke dem, han da skal sende dem en Frelser og en mægtig og udfri dem.
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
21 Og Herren skal kendes af Ægypten, og Ægypterne skulle kende Herren paa den Dag, og de skulle tjene ham med Slagtoffer og Madoffer og love Herren Løfte og betale det.
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
22 Og Herren skal slaa Ægypten, ja, slaa og læge; og de skulle vende om til Herren, og han skal bønhøre dem og læge dem.
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
23 Paa denne Dag skal der være en banet Vej fra Ægypten til Assyrien, og Assyrerne skulle komme til Ægypten og Ægypterne til Assyrien, og Ægypterne tillige med Assyrerne skulle tjene Herren.
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
24 Paa denne Dag skal Israel være selv tredje med Ægypterne og Assyrerne, en Velsignelse midt paa Jorden,
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
25 hvilke den Herre Zebaoth har velsignet, sigende: Velsignet være mit Folk, Ægypterne, og mine Hænders Gerning, Assyrerne, og min Arv, Israel!
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”

< Esajas 19 >