< Esajas 14 >
1 Thi Herren skal forbarme sig over Jakob og atter udvælge Israel og lade dem bosætte sig i deres Land; og den fremmede skal slutte sig til dem og holde sig til Jakobs Hus.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 Og Folkene skulle tage dem og føre dem til deres Hjem, og Israels Hus skal tage hine til Eje som Tjenere og Tjenestepiger i Herrens Land og holde dem fangne, som havde fanget dem selv, og regere over sine Undertrykkere.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 Og det skal ske paa den Dag, naar Herren skaffer dig Rolighed efter din Møje og din Uro og efter den haarde Trældom, med hvilken man lod dig trælle:
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 Da skal du istemme denne Sang imod Kongen af Babel og sige: Hvorledes er Undertrykkeren hørt op! hvorledes er Trykket hørt op!
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 Herren har sønderbrudt de ugudeliges Stav, Herskernes Spir,
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 som slog Folkene i Grumhed med Slag uden Afladelse og regerede over Folkefærd i Vrede, med skaanselløs Forfølgelse.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 Al Jorden hviler og er stille, de raabe med frydefuldt Skrig.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Cypresserne glæde sig ogsaa over dig, ja, Cedrene paa Libanon, og sige: Fra den Tid, du ligger, kommer ingen op at omhugge os.
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Dødsriget her neden til bæver for dig, for at møde dig, naar du kommer, det bringer Dødningerne til at rejse sig for din Skyld, alle Jordens mægtige, det lader alle Folkekongerne staa op fra deres Troner. (Sheol )
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol )
10 Alle svare de og sige til dig: Du er og bleven afmægtig som vi, du er bleven os lig!
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Din Højhed med dine Psaltres Brusen er nedkastet til Dødsriget; Orme bredes under dig, og Maddiker bedække dig. (Sheol )
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol )
12 Hvorledes er du falden ned fra Himmelen, du Morgenstjerne, du Morgenrødens Søn? hvorledes er du nedhugget til Jorden, du, som nedtraadte Folkefærd?
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Og du sagde i dit Hjerte: Jeg vil stige op til Himmelen, ophøje min Trone over Guds Stjerner, og jeg vil sidde paa Forsamlingsbjerget, yderst imod Norden;
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 jeg vil fare op over de højeste Skyer, jeg vil være den Højeste lig!
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Men til Dødsriget skal du nedfare, til Hulens nederste Steder! (Sheol )
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol )
16 Hvo dig ser, skal stirre paa dig, de skulle betragte dig og sige: Mon denne være den Mand, som bragte Jorden til at bæve? som bragte Rigerne til at skælve?
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 som gjorde Jorderige til en Ørk og nedbrød dets Stæder? som ikke løste sine bundne for at lade dem gaa hjem?
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 Alle Folkenes Konger, de ligge alle med Ære, hver i sit Hus;
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 men du, du er henslængt, uden Grav, som en vederstyggelig Kvist, bedækket med ihjelslagne, som ere gennemborede med Sværd, som fore ned i Stenhulens Dyb; du er som et nedtraadt Aadsel.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 Du skal ikke forenes med dem ved Begravelse; thi du har ødelagt dit Land, ihjelslaget dit Folk; de ondes Sæd skal ikke nævnes evindelig.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Bereder hans Børn et Blodbad for deres Fædres Misgerning, at de ikke rejse sig, hverken til at arve Jorden eller til at fylde Jorderiges Kreds med Stæder.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 Thi jeg vil staa op imod dem, siger den Herre Zebaoth, og udrydde Babels Navn og hans overblevne og Søn og Sønnesøn, siger Herren.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 Og jeg vil gøre den til Bo for Pindsvin og til Vandsumpe og feje den bort med Ødelæggelsens Kost, siger den Herre Zebaoth.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 Den Herre Zebaoth har svoret og sagt: Sandelig, som jeg har tænkt, skal det ske, og som jeg har besluttet, skal det staa fast:
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 At jeg skal sønderknuse Assur i mit Land og nedtræde ham paa mine Bjerge, saa at hans Aag skal tages fra dem, og hans Byrde vige fra deres Skuldre!
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 Dette er det Raad, som er besluttet over den hele Jord, og dette er den Haand, som er udrakt over alle Folkefærd.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Thi den Herre Zebaoth har besluttet det, og hvo vil gøre det til intet? og hans Haand er udrakt, og hvo vil afvende den?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 I det Aar, der Kong Akas døde, skete denne Profeti.
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Glæd dig ikke, du ganske Filisterland! at hans Stav, som slog dig, er sønderbrudt; thi af Slangens Rod skal udgaa en Basilisk, og dens Frugt skal blive en flyvende Drage.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 Og de førstefødte af de ringe skulle finde Næring og de fattige ligge tryggelig; men jeg vil døde din Rod med Hunger, og man skal ihjelslaa de overblevne af dig.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Hyl, Port! skrig, Stad! vær mistrøstig, du ganske Filisterland! thi der skal komme en Røg af Norden, og der er ingen Efternøler i hans Skarer.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 Og hvad skal man svare Folkets Bud? — At Herren har grundfæstet Zion, og at de elendige af hans Folk skulle have Tilflugt i den.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”