< Esajas 10 >

1 Ve dem, som give ugudelige Love og udstede uretfærdige Skrivelser
Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
2 for at fortrænge de ringe fra deres Ret og for at fravende de elendige iblandt mit Folk deres Ret, at Enkerne maa være deres Bytte, og at de kunne berøve de faderløse!
don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
3 Men hvad ville I gøre imod Hjemsøgelsens Dag og imod den Ødelæggelse, som skal komme langt borte fra? til hvem ville I fly om Hjælp? og hvor ville I lade eders Herlighed blive?
Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
4 Enhver, som ikke maa bøje sig iblandt de bundne, skal falde iblandt de ihjelslagne. Med alt dette har hans Vrede ikke lagt sig; men hans Haand er endnu udrakt.
Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
5 Ve Assur, min Vredes Ris! min Harme er Kæppen i hans Haand.
“Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
6 Jeg sender ham imod et vanhelligt Folk og giver ham Befaling imod det Folk, som jeg er vred paa, til at gøre Bytte og røve Rov og til at træde det ned som Ler paa Gader.
Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
7 Men han, han mener det ikke saa, og hans Hjerte tænker ikke saa; men hans Hu staar til at ødelægge og at udrydde ikke faa Folk.
Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
8 Thi han siger: Ere mine Fyrster ikke Konger til Hobe?
Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
9 Er det ikke gaaet Kalno som Karkemis? ikke Hamath som Arpad? ikke Samaria som Damaskus?
‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
10 Ligesom min Haand har ramt Afgudernes Riger, hvor der var flere Billeder end i Jerusalem og i Samaria:
Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
11 Mon jeg ikke, saaledes som jeg har gjort ved Samaria og dens Afguder, saaledes skal gøre ved Jerusalem og ved dens Afguder?
ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
12 Og det skal ske, naar Herren har udrettet al sin Gerning paa Zions Bjerg og i Jerusalem, da vil jeg hjemsøge Kongen af Assyriens Hovmods Frugt og hans Hoffærdigheds Pragt.
Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
13 Fordi han siger: Ved min Haands Kraft har jeg gjort det og ved min Visdom, thi jeg er forstandig; og jeg borttager Folkenes Landemærker og har røvet deres Forraad, og som den mægtige nedkaster jeg dem, som sidde i Højsædet.
Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
14 Og min Haand har fundet hen til Folkenes Gods som til en Fuglerede, og jeg har sanket alt Landet, som man sanker Æg, der ere forladte; og der var ingen, som rørte en Vinge, eller som oplod Næbet og peb.
Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
15 Kan vel Øksen rose sig imod den, som hugger med den? eller Saven trodse den, som trækker den? som om en Stav vilde svinge den, som opløfter den, eller som om en Kæp vilde opløfte den, som ikke er Træ?
Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
16 Derfor skal Herren, den Herre Zebaoth, sende Magerhed paa hans fede, og under hans Herlighed skal der brænde et Baal som et brændende Baal.
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
17 Og Israels Lys skal vorde en Ild, og hans Hellige skal vorde en Lue; og den skal brænde og fortære hans Torn og Tidsler paa een Dag.
Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
18 Og hans Skovs og hans Frugthaves Herlighed skal den fortære med Rub og Stub; og han skal blive som en syg, der vansmægter.
Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
19 Og de overblevne Træer i hans Skov skulle være faa i Tal, og et Barn skal kunne opskrive dem.
Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
20 Og det skal ske paa den Dag, da skulle de overblevne i Israel og de undkomne af Jakobs Hus ikke mere forlade sig paa den, som slaar det; men de skulle forlade sig paa Herren, Israels Hellige, i Oprigtighed.
A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
21 De overblevne skulle omvende sig, de overblevne af Jakob, til den vældige Gud.
Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
22 Thi om dit Folk, o Israel! er som Havets Sand, skulle kun de overblevne deraf omvende sig; Fordærvelsen er bestemt, den breder sig ud med Retfærdighed som en Strøm.
Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
23 Thi Fordærvelsen og det besluttede Raad skal Herren, den Herre Zebaoth, udføre, midt i hele Landet.
Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
24 Derfor, saa siger Herren, den Herre Zebaoth: Frygt ikke, mit Folk! du, som bor i Zion, for Assur; han slaar dig med Staven og opløfter sin Kæp over dig, paa samme Vis som Ægypterne.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
25 Thi endnu et lidet, en føje Tid, saa skal Fortørnelsen endes, og min Vrede komme for at fortære dem.
Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
26 Og den Herre Zebaoth skal svinge en Svøbe over ham, som da Midian blev slaaet paa Orebs Klippe, og sin Stav, som han hævede over Havet, den skal han opløfte paa samme Vis som i Ægypten.
Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
27 Og det skal ske paa den Dag, da skal hans Byrde borttages fra dine Skuldre og hans Aag fra din Hals; og Aaget skal sprænges for Fedmens Skyld.
A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
28 Han kommer over Ajat, han drager igennem Migron, han lader sit Tros blive tilbage i Mikmas.
Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
29 De drage igennem Passet, de blive Natten over i Geba; Rama bæver, Sauls Gibea flyr.
Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
30 Raab højt, du Gallims Datter! giv Agt, Lajsa! ulykkeligt er Anathoth.
Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
31 Madmena flygter, Indbyggerne i Gebim samle sig til Flugt.
Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
32 Endnu bliver han staaende denne Dag i Nob; saa løfter han sin Haand imod Zions Hus's Bjerg, imod Jerusalems Høj.
A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
33 Se, Herren, den Herre Zebaoth, skal nedhugge de skønne Grene, saa man gruer; og de ranke Stammer skulle afhugges, og de høje skulle blive lave.
Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
34 Og den tykke Skov nedhugges med Jernet, og Libanon falder for den Mægtige.
Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.

< Esajas 10 >