< Hoseas 8 >
1 Basunen for din Gane! Som en Ørn over Herrens Hus! fordi de have overtraadt min Pagt og forbrudt sig imod min Lov.
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2 Til mig raabe de: Min Gud! vi, Israel, kende dig.
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3 Israel har forkastet det gode; Fjenden forfølge ham!
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 De have indsat Konger, men ikke fra mig; de have indsat Fyrster, men jeg vidste det ikke; de have gjort sig Afguder af deres Sølv og deres Guld, for at det kan udryddes.
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 Din Kalv, Samaria! er forkastet, min Vrede er optændt imod dem, hvor længe? de taale ikke Renhed.
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 Thi af Israel er ogsaa den, en Mester har gjort den, og den er ikke en Gud; men til Splinter bliver Samarias Kalv.
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 Thi Vind saa de, og Storm høste de; Korn paa Roden have de ej, Grøden giver ikke Mel, og om den end giver det, skulle fremmede opsluge det.
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 Opslugt er Israel; nu ere de blevne iblandt Hedningerne som et Kar, hvortil ingen har Lyst.
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 Thi de droge op til Assyrien som et Vildæsel, der gaar sine egne Veje; Efraim tingede om Elskov.
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 Men tinge de iblandt Folkene, saa vil jeg dog nu samle dem; og de skulle begynde at mindskes under Trykket af Fyrsternes Konge.
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 Thi Efraim byggede mange Altre til at synde ved; han har faaet Altre til at synde ved.
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 Jeg skriver ham mine mangfoldige Love; de ere blevne agtede som noget fremmed.
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 Som Ofre, de bringe mig, ofre de Kød og æde; Herren finder ikke Behag i dem; nu vil han komme deres Misgerning i Hu og hjemsøge deres Synder; de skulle komme tilbage til Ægypten.
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 Og Israel forglemte sin Skaber og byggede Paladser, og Juda opførte mange faste Stæder; men jeg vil sende Ild i hans Stæder, og den skal fortære hans Paladser.
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”