< Hoseas 1 >

1 Herrens Ord, som kom til Hoseas, Beeris Søn, i de Dage, da Ussias, Jotham, Akas, Ezekias vare Konger i Juda, og i de Dage, da Jeroboam, Joas's Søn, var Konge i Israel.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
2 Der Herren begyndte at tale ved Hoseas, da sagde Herren til Hoseas: Gak hen, tag dig en Horkvinde og Horebørn, thi Hor bedriver Landet ved at vende sig bort fra Herren.
Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
3 Og han gik og tog Gomer, Diblajims Datter, og hun undfangede og fødte ham en Søn.
Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
4 Og Herren sagde til ham: Kald hans Navn Jisreel; thi endnu en lille Stund, saa vil jeg hjemsøge Jisreels Blodskyld over Jehus Hus og gøre Ende paa Israels Hus's Rige.
Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
5 Og det skal ske paa denne Dag, da vil jeg sønderbryde Israels Bue i Jisreels Dal.
A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
6 Og hun undfangede atter og fødte en Datter; og han sagde til ham: Kald hendes Navn Lo-Rukama; thi jeg vil ikke ydermere forbarme mig over Israels Hus, saa at jeg skulde tilgive dem.
Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
7 Dog vil jeg forbarme mig over Judas Hus og frelse dem ved Herren deres Gud; men jeg vil ikke frelse dem ved Bue eller ved Sværd eller ved Krig, ved Heste eller ved Ryttere.
Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
8 Og hun afvante Lo-Rukama, og hun undfangede og fødte en Søn.
Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
9 Og han sagde: Kald hans Navn Lo-Ammi; thi I ere ikke mit Folk, og jeg vil ikke være eders.
Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
10 Dog skal Israels Børns Tal blive som Havets Sand, der ikke kan maales og ikke tælles; og det skal ske, at paa det Sted, hvor der siges til dem: I ere ikke mit Folk, der skal der siges til dem: Den levende Guds Børn.
“Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
11 Og Judas Børn og Israels Børn skulle samles til Hobe og sætte sig eet Overhoved og drage op af Landet; thi stor er Jisreels Dag.
Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.

< Hoseas 1 >