< Hebræerne 7 >

1 Thi denne Melkisedek, Konge i Salem, den højeste Guds Præst, som gik Abraham i Møde, da han vendte tilbage fra Kongernes Nederlag, og velsignede ham,
Wannan Melkizedek sarkin Salem ne da kuma firist na Allah Mafi Ɗaukaka. Shi ne ya sadu da Ibrahim ya albarkace shi sa’ad da Ibrahim ya dawowa daga cin nasara a bisa sarakuna,
2 hvem ogsaa Abraham gav Tiende af alt, og som, naar hans Navn udlægges, først er Retfærdigheds Konge, dernæst ogsaa Salems Konge, det er: Freds Konge,
Ibrahim kuwa ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome. Ma’anar sunan Melkizedek ita ce, “sarkin adalci.” Amma da yake Salem yana nufin “salama,” shi kuma “Sarkin salama” ne.
3 uden Fader, uden Moder, uden Slægtregister, uden Dages Begyndelse og uden Livs Ende, men gjort lig med Guds Søn, han forbliver Præst for bestandig.
Ba shi da mahaifi ko mahaifiya, ba shi da asali, ba shi da farko ko ƙarshe, shi dai kamar Ɗan Allah ne kuma firist ne har abada.
4 Ser dog, hvor stor denne er, hvem endog Patriarken Abraham gav Tiende af Byttet.
Ku dubi irin girman da Melkizedek mana. Ko kakanmu Ibrahim ma ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na ganima!
5 Og hine, som, idet de høre til Levi Sønner, faa Præstedømmet, have et Bud om at tage Tiende efter Loven af Folket, det er af deres Brødre, endskønt disse ere udgaaede af Abrahams Lænd;
Yanzu doka ta umarci zuriyar Lawi waɗanda suka zama firistoci su karɓi kashi ɗaya bisa goma daga wurin mutane, wato,’yan’uwansu, ko da yake’yan’uwansu zuriyar Ibrahim ne.
6 men han, som ikke regner sin Slægt fra dem, har taget Tiende af Abraham og har velsignet den, som havde Forjættelserne.
Ko da yake Melkizedek ba daga zuriyar Lawi ba ne, duk da haka Ibrahim ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na abin da yake da shi, Melkizedek kuwa ya sa masa albarka, shi da aka yi wa alkawura.
7 Men uden al Modsigelse er det den ringere, som velsignes af den ypperligere.
Kowa ya sani cewa na gaba shi yake sa wa na baya albarka.
8 Og her er det dødelige Mennesker, som tage Tiende; men der er det en, om hvem der vidnes, at han lever.
Firistoci ake ba wa kashi ɗaya bisa goma na abin da mutane suke samu. Amma dukan firistoci sukan mutu, sai dai Melkizedek, kuma nassi ya ce yana da rai.
9 Ja, saa at sige, har endog Levi, som tager Tiende, igennem Abraham givet Tiende;
Ana ma iya cewa zuriyar Lawi, mai karɓar kashi ɗaya bisa goma daga mutane, ya ba da kashi ɗaya bisa goma ta wurin Ibrahim,
10 thi han var endnu i Faderens Lænd, da Melkisedek gik denne i Møde.
wannan ya kasance haka domin an haifi Lawi daga baya a iyalin Ibrahim wanda ya ba wa Melkizedek kashi ɗaya bisa goma.
11 Hvis der altsaa var Fuldkommelse at faa ved det levitiske Præstedømme (thi paa Grundlag af dette har jo Folket faaet Loven), hvilken Trang var der da yderligere til, at en anden Slags Præst skulde opstaa efter Melkisedeks Vis og ikke nævnes efter Arons Vis?
Ko da yake Dokar Musa ta ce dole firistoci su kasance zuriyar Lawi, waɗannan firistoci ba su iya sa wani yă zama cikakke ba. Saboda akwai bukata wani firist kamar Melkizedek ya zo, a maimakon wani daga iyalin Haruna.
12 Naar nemlig Præstedømmet omskiftes, sker der med Nødvendighed ogsaa en Omskiftelse af Loven.
Gama in aka canja yadda ake zaɓan firist, dole a canja Dokar ita ma.
13 Thi han, om hvem dette siges, har hørt til en anden Stamme, af hvilken ingen har taget Vare paa Alteret.
Mutumin da muke wannan zance a kai, ai, shi na wata kabila ce dabam, wadda ba wani daga kabilar da ya taɓa yin hidima a bagade.
14 Thi det er vitterligt, at af Juda er vor Herre oprunden, og for den Stammes Vedkommende har Moses intet talt om Præster.
Kowa ya san cewa Ubangijinmu ya fito ne daga zuriyar Yahuda ne, kuma Musa bai taɓa ce firistoci za su fito daga wannan kabila ba.
15 Og det bliver end ydermere klart, naar der i Lighed med Melkisedek opstaar en anden Slags Præst,
Canjin nan a Dokar Allah ya ƙara fitowa fili da wani firist dabam wanda yake kamar Melkizedek ya bayyana.
16 som ikke er bleven det efter et kødeligt Buds Lov, men efter et uopløseligt Livs Kraft.
Ya zama firist ne ba saboda ya cika wata ƙa’ida ta zama zuriyar Lawi ba, sai dai bisa ga ikon ran da ba a iya hallakawa.
17 Thi han faar det Vidnesbyrd: „Du er Præst til evig Tid efter Melkisedeks Vis.” (aiōn g165)
Gama nassi ya ce, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn g165)
18 Thi vel sker der Ophævelse af et forudgaaende Bud, fordi det var svagt og unyttigt
Ta haka aka kawar da ƙa’ida marar ƙarfi da kuma marar amfani
19 (thi Loven har ikke fuldkommet noget); men der sker Indførelse af et bedre Haab, ved hvilket vi nærme os til Gud.
(gama doka ba tă mai da wani abu cikakke ba), yanzu kuwa bege mafi kyau ya ɗauki matsayinta. Ta haka kuma muka matso kusa da Allah.
20 Og saa vist som det ikke er sket uden Ed,
Ba kuwa da rashin rantsuwa aka yi haka ba. Waɗansu sun zama firistocin ba tare da wata rantsuwa ba,
21 (thi hine ere blevne Præster uden Ed, men denne med Ed, ved den, som siger til ham: „Herren svor, og han skal ikke angre det: Du er Præst til evig Tid”): (aiōn g165)
shi wannan ya zama firist ta wurin rantsuwar da Allah ya yi da ya ce masa, “Ubangiji ya rantse, ba kuwa zai canja zuciyarsa ba, ‘Kai firist ne na har abada.’” (aiōn g165)
22 Saa vist er Jesus bleven Borgen for en bedre Pagt.
Saboda wannan rantsuwa, Yesu ya zama tabbacin alkawari mafi kyau.
23 Og hine ere blevne Præster, flere efter hinanden, fordi de ved Døden hindredes i at vedblive;
To, akwai waɗannan firistoci da yawa, da yake mutuwa ta hana su cin gaba da aikin zaman firist;
24 men denne har et uforgængeligt Præstedømme, fordi han bliver til evig Tid, (aiōn g165)
amma Yesu ba zai mutu ba, don haka zai zama firist har abada. (aiōn g165)
25 hvorfor han ogsaa kan fuldkomment frelse dem, som komme til Gud ved ham, efterdi han lever altid til at gaa i Forbøn for dem.
Saboda haka ya iya ba da ceto gaba ɗaya ga masu zuwa wurin Allah ta wurinsa, gama kullum a raye yake saboda yă yi roƙo dominsu.
26 Thi en saadan Ypperstepræst var det ogsaa, som sømmede sig for os, en from, uskyldig, ubesmittet, adskilt fra Syndere og ophøjet over Himlene;
Irin wannan babban firist ne muke bukata, shi mai tsarki ne, marar aibi, mai tsabta, ba kamar mu masu zunubi ba sam. An ɗaukaka shi fiye da kome a sama.
27 en, som ikke hver Dag har nødig, som Ypperstepræsterne, at frembære Ofre først for sine egne Synder, derefter for Folkets; thi dette gjorde han een Gang for alle, da han ofrede sig selv.
Ba ya bukata yă yi ta miƙa hadayu kowace rana saboda zunubansa, sa’an nan saboda zunuban mutane kamar sauran firistoci. Ya miƙa hadaya sau ɗaya tak, sa’ad da ya miƙa kansa.
28 Thi Loven indsætter til Ypperstepræster Mennesker, som have Skrøbelighed; men Edens Ord, som kom senere end Loven, indsætter en Søn, som er fuldkommet til evig Tid. (aiōn g165)
Gama doka takan naɗa babban firist a cikin mutane masu kāsawa; amma rantsuwar da ta zo bayan dokar, ta naɗa Ɗan, wanda aka mai da shi cikakke har abada. (aiōn g165)

< Hebræerne 7 >