+ 1 Mosebog 1 >
1 I Begyndelsen skabte Gud Himmelen og Jorden.
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2 Og Jorden var øde og tom, og der var Mørke oven over Afgrunden, og Guds Aand svævede oven over Vandene.
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3 Og Gud sagde: Der vorde Lys; og der blev Lys.
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
4 Og Gud saa, at Lyset var godt, og Gud gjorde Skilsmisse imellem Lyset og Mørket.
Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5 Og Gud kaldte Lyset Dag, og Mørket kaldte han Nat; og der blev Aften, og der blev Morgen, første Dag.
Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
6 Og Gud sagde: Der vorde en udstrakt Befæstning midt i Vandene, og den skal skille imellem Vand og Vand.
Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
7 Og Gud gjorde den udstrakte Befæstning og gjorde Skilsmisse imellem Vandet, som var nedentil i den udstrakte Befæstning, og imellem Vandet, som var oventil i den udstrakte Befæstning; og det skete saa.
Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
8 Og Gud kaldte den udstrakte Befæstning Himmel; og der blev Aften, og der blev Morgen, anden Dag.
Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
9 Og Gud sagde: Vandene under Himlene samle sig til eet Sted, at det tørre ses; og det skete saa.
Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
10 Og Gud kaldte det tørre Jord, og Vandenes Samling kaldte han Hav; og Gud saa, at det var godt.
Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
11 Og Gud sagde: Jorden lade fremvokse Græs, Urter, som give Sæd, frugtbare Træer, som bære Frugt efter sit Slags og have sin Sæd i sig paa Jorden; og det skete saa.
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
12 Og Jorden frembragte Græs, Urter, som gave Sæd efter sit Slags, og Træer, som bare Frugt og havde sin Sæd i sig efter sit Slags; og Gud saa, at det var godt.
Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
13 Og der blev Aften, og der blev Morgen, tredje Dag.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
14 Og Gud sagde: Der vorde Lys paa Himmelens udstrakte Befæstning, at gøre Skilsmisse imellem Dagen og imellem Natten; og de skulle være til Tegn og til bestemte Tider og til Dage og Aar.
Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
15 Og de skulle være til Lys paa Himmelens udstrakte Befæstning til at lyse over Jorden; og det skete saa.
bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
16 Og Gud gjorde de to store Lys, det store Lys at regere Dagen og det lille Lys at regere Natten og Stjernerne.
Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
17 Og Gud satte dem paa Himmelens udstrakte Befæstning til at lyse over Jorden
Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
18 og til at regere om Dagen og om Natten og til at skille imellem Lyset og imellem Mørket; og Gud saa, at det var godt.
su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
19 Og der blev Aften, og der blev Morgen, fjerde Dag.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
20 Og Gud sagde: Vandet vrimle med en Vrimmel af levende Væsener, og Fugle skulle flyve over Jorden imod Himmelens udstrakte Befæstning.
Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
21 Og Gud skabte de store Havdyr og alle Haande levende Væsener, som krybe, hvilke vrimle i Havet, efter sit Slags og alle Haande Fugle med Vinger efter sit Slags; og Gud saa, at det var godt.
Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
22 Og Gud velsignede dem og sagde: Vorder frugtbare og mangfoldige, og fylder Vandene i Havet, og Fuglene vorde mangfoldige paa Jorden.
Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
23 Og der blev Aften, og der blev Morgen, femte Dag.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
24 Og Gud sagde: Jorden frembringe levende Dyr efter sit Slags, Fæ og Kryb og vilde Dyr paa Jorden efter sit Slags; og det skete saa.
Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
25 Og Gud gjorde vilde Dyr paa Jorden efter sit Slags og Fæ efter sit Slags og alle Haande Kryb paa Jorden efter sit Slags; og Gud saa, at det var godt.
Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
26 Og Gud sagde: Lader os gøre et Menneske i vort Billede, efter vor Lignelse; og de skulle regere over Havets Fiske og over Himmelens Fugle og over Fæet og over al Jorden og over alt Kryb, som kryber paa Jorden.
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
27 Og Gud skabte Mennesket i sit Billede, han skabte det i Guds Billede; Mand og Kvinde skabte han dem.
Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
28 Og Gud velsignede dem, og Gud sagde til dem: Vorder frugtbare og mangfoldige, og opfylder Jorden, og gører eder den underdanig, og regerer over Havets Fiske og over Himmelens Fugle og over hvert Dyr, som kryber paa Jorden.
Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
29 Og Gud sagde: Se, jeg har givet eder alle Urter, som give Sæd, som ere over al Jorden, og alle Haande Træer, i hvilke er Træers Frugt, som have Sæd; de skulle være eder til Føde.
Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
30 Og alle Dyr paa Jorden og alle Fugle under Himmelen og alt Kryb paa Jorden, i hvilke er en levende Sjæl, har jeg givet alle Haande grønne Urter til at æde; og det skete saa.
Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
31 Og Gud saa alt det, han havde gjort, og se, det var meget godt; og der blev Aften, og der blev Morgen, den sjette Dag.
Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.