< 1 Mosebog 50 >

1 Da faldt Josef over sin Faders Ansigt og græd over ham og kyssede ham.
Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
2 Og Josef befalede sine Tjenere, Lægerne, at balsamere hans Fader; saa balsamerede Lægerne Israel.
Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
3 Og fyrretyve Dage medgik hertil; thi saa mange Dage medgaa til Balsameringen; og Ægypterne begræd ham halvfjerdsindstyve Dage.
Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
4 Og der Grædedagene over ham vare forbi, da talede Josef til Faraos Hus og sagde: Kære, dersom jeg har fundet Naade for eders Øjne, da taler, kære, for Faraos Øren og siger:
Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
5 Min Fader tog en Ed af mig og sagde: Se, jeg dør; i min Grav, som jeg lod mig grave i Kanaans Land, der skal du begrave mig; og nu, kære, vil jeg drage op og begrave min Fader, og jeg vil komme igen.
‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
6 Og Farao sagde: Drag op og begrav din Fader, saaledes som han tog Ed af dig.
Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
7 Og Josef drog op for at begrave sin Fader, og alle Faraos Tjenere fore op med ham, de ældste af hans Hus, og alle de ældste af Ægyptens Land,
Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
8 og Josefs ganske Hus og hans Brødre og hans Faders Hus, kun deres smaa Børn og deres Faar og deres Øksne lode de blive i Gosen Land.
da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
9 Og baade Vogne og Ryttere droge op med ham, og det var en meget stor Hær.
Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
10 Der de kom til den Lade Atad, som ligger paa hin Side Jordan, da holdt de der en stor og saare svar Klage, og han lod holde Sorrig for sin Fader syv Dage.
Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
11 Og Kananiten, som boede i Landet, saa den Sorrig ved den Lade Atad, og de sagde: Denne er en svar Sorrig for Ægypterne; derfor kaldte man det Steds Navn: Ægypternes Sorrig, som er paa hin Side Jordan.
Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
12 Og hans Sønner gjorde saaledes med ham, som han havde befalet dem.
Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
13 Og hans Sønner førte ham til Kanaans Land og begrove ham i Hulen paa den Ager Makpela, den Ager, som Abraham havde købt til Begravelses Ejendom af Efron den Hethiter, tvært over for Mamre.
Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
14 Og Josef kom igen til Ægypten, han og hans Brødre og alle de, som vare dragne op med ham til at begrave hans Fader, efter at han havde begravet sin Fader.
Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
15 Der Josefs Brødre saa, at deres Fader var død, da sagde de: Maaske Josef hader os, saa han visselig vil betale os igen alt det onde, som vi have gjort imod ham.
Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
16 Og de beskikkede nogen at tale til Josef, sigende: Din Fader befalede, før han døde og sagde:
Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
17 Saa skulle I sige til Josef: Kære, forlad dog dine Brødre deres Overtrædelse og deres Synd, at de gjorde ilde imod dig; kære, saa forlad nu din Faders Guds Tjenere deres Overtrædelse; da græd Josef, der de talede til ham.
Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
18 Og hans Brødre gik ogsaa selv hen og faldt ned for hans Ansigt og sagde: Se, vi ere dine Tjenere!
’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
19 Og Josef sagde til dem: Frygter ikke; thi monne jeg være i Guds Sted?
Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
20 Og I tænkte ondt imod mig; Gud tænkte at vende det til det gode, for at gøre, hvad der sker paa denne Dag, at holde meget Folk ved Live.
Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
21 Saa frygter nu ikke, jeg vil opholde eder og eders smaa Børn; saa trøstede han dem og talede kærlig med dem.
Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
22 Saa boede Josef i Ægypten, han og hans Faders Hus, og Josef levede hundrede og ti Aar.
Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
23 Og Josef saa Efraims Sønner i tredje Led; desligeste Makirs, Manasse Søns, Sønner bleve fødte paa Josefs Knæ.
Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
24 Og Josef sagde til sine Brødre: Jeg dør, og Gud skal visselig besøge eder og føre eder op af dette Land, til det Land, som han har tilsvoret Abraham, Isak og Jakob.
Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
25 Og Josef tog en Ed af Israels Børn og sagde: Gud skal visselig besøge eder, og I skulle føre mine Ben op herfra.
Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
26 Saa døde Josef hundrede og ti Aar gammel; og de balsamerede ham, og man lagde ham i Kiste i Ægypten.
Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.

< 1 Mosebog 50 >