< 1 Mosebog 47 >

1 Og Josef kom og forkyndte Farao det og sagde: Min Fader og mine Brødre og deres Faar og deres Øksne og alt det, de have, ere komne fra Kanaans Land; og se, de ere i Gosen Land.
Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
2 Og af samtlige sine Brødre tog han fem Mænd og stillede dem for Farao.
Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
3 Da sagde Farao til hans Brødre: Hvad er eders Haandtering? og de sagde til Farao: Dine Tjenere ere Faarehyrder, baade vi og vore Fædre.
Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
4 Og de sagde til Farao: Vi ere komne at være fremmede i Landet; thi der er ingen Føde til det Kvæg, som dine Tjenere have; thi Hungeren er svar i Kanaans Land; og nu, kære, lad dine Tjenere bo i Gosen Land.
Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
5 Og Farao talede til Josef og sagde: Din Fader og dine Brødre ere komne til dig.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
6 Ægyptens Land ligger for dig, lad din Fader og dine Brødre bo paa det bedste Sted i Landet, lad dem bo i Gosen Land, og dersom du ved, at der er duelige Mænd iblandt dem, da sæt dem til Opsynsmænd over Kvæget, over det, som jeg har.
ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
7 Og Josef førte Jakob sin Fader ind og stillede ham for Faraos Ansigt, og Jakob velsignede Farao.
Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
8 Og Farao sagde til Jakob: Hvor gammel er du?
sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
9 Og Jakob sagde til Farao: Min Udlændigheds Aars Dage ere hundrede og tredive Aar; faa og onde have mit Livs Aars Dage været og have ikke naaet til mine Fædres Livs Aars Dage i deres Udlændigheds Dage.
Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
10 Og Jakob velsignede Farao og gik ud fra Farao.
Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
11 Men Josef lod sin Fader og sine Brødre bo og gav dem Ejendom i Ægyptens Land, paa det bedste Sted i Landet, i det Land Raamses, som Farao havde befalet.
Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
12 Og Josef underholdt sin Fader og sine Brødre og alt sin Faders Hus med Brød til de smaa Børns Mund.
Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
13 Og der var ikke Brød i alt Landet; thi Hungeren var saare svar, saa at Ægyptens Land og Kanaans Land forsmægtede for Hungerens Skyld.
A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
14 Og Josef samlede alle Pengene, som fandtes i Ægyptens Land og i Kanaans Land, for det Korn, som de købte, og Josef lod Pengene komme i Faraos Hus.
Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
15 Og da det var forbi med Pengene i Ægyptens Land og i Kanaans Land, da kom alle Ægypterne til Josef og sagde: Fly os Brød, og hvi skulle vi dø for dig? thi Pengene ere borte.
Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
16 Og Josef sagde: Flyr hid eders Kvæg, saa vil jeg give eder Brød for eders Kvæg, dersom Pengene ere borte.
Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
17 Saa førte de deres Kvæg til Josef, og Josef gav dem Brød for Hestene og for Kvæget, som de ejede, og for Øksnene, som de ejede, og for Asenerne; saa hjalp han dem med Brød for alt deres Kvæg i det samme Aar.
Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
18 Der det samme Aar havde Ende, da kom de i det andet Aar til ham og sagde til ham: Vi ville ikke dølge for min Herre, at ikke alene Pengene ere borte, men og Kvæget, som vi ejede, er kommet til min Herre; vi have intet tilbage til min Herre, uden vore Legemer og vor Jord.
Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
19 Hvi skulle vi dø for dine Øjne, baade vi og tilmed vor Jord blive øde? køb os og vor Jord for Brød; og vi med vor Jord ville være Faraos Tjenere, og giv os Sæd, at vi maa leve og ikke dø, og Jorden ikke blive øde.
Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
20 Og Josef købte af Ægyptens Jord til Farao; thi Ægypterne solgte hver sin Ager, fordi Hungeren var svar over dem; og Landet blev Faraos.
Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
21 Og han lod Folket flytte om i Stæderne, fra den ene Ende af Ægyptens Land til den anden.
Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
22 Alene Præsternes Jord købte han ikke; thi Præsterne havde deres beskikkede Del af Farao; og de aade deres beskikkede Del, som Farao havde givet dem, derfor solgte de ikke deres Jord.
Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
23 Da sagde Josef til Folket: Se, jeg har i Dag købt eder og eders Jord til Farao, se, der have I Sæd, og I skulle besaa Jorden.
Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
24 Og med Afgrøden skal det være saaledes, at I skulle give Farao den femte Part, og de fire Parter skulle I beholde til Sæd til Ageren og til Spise for eder og for dem, som ere i eders Huse, og til eders smaa Børn at æde.
Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
25 Og de sagde: Du har holdt os ved Live, lad os finde Naade for min Herres Øjne, og vi ville være Faraos Trælle.
Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
26 Saa gjorde Josef det til en Skik indtil denne Dag over Ægyptens Jord, at Farao skal have den femte Part; ikkun Præsternes Jord, den alene, blev ikke Faraos.
Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
27 Og Israel boede i Ægyptens Land, i Gosen Land; og de fik Ejendom der og vare frugtbare og bleve saare mangfoldige.
To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
28 Og Jakob levede i Ægyptens Land sytten Aar; og Jakobs Dage, hans Livs Aar, vare hundrede og syv og fyrretyve Aar.
Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
29 Og Israels Dage kom nær, at han skulde dø, og han kaldte ad sin Søn Josef og sagde til ham: Kære, dersom jeg har fundet Naade for dig, da læg, kære, din Haand under min Lænd, og bevis den Miskundhed og Troskab mod mig, at du, kære, ikke begraver mig i Ægypten.
Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
30 Og jeg vil ligge hos mine Fædre, og du skal føre mig af Ægypten og begrave mig i deres Grav; og han sagde: Jeg vil gøre, som du har sagt.
amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
31 Men han sagde: Sværg mig; og han svor ham; og Israel bøjede sig over Hovedgærdet i Sengen.
Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.

< 1 Mosebog 47 >