< 1 Mosebog 40 >
1 Og det hændte sig derefter, at Kongen af Ægyptens Mundskænk og Bager syndede mod deres Herre, Kongen af Ægypten.
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 Og Farao blev vred paa begge sine Betjente, paa den øverste Mundskænk og den øverste Bager.
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 Og han satte dem i Forvaring i Huset hos Øversten for Livvagten, i Fængslets Hus, paa det Sted, hvor Josef var Fange.
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 Og Øversten for Livvagten beskikkede Josef til at være hos dem, og han betjente dem, og de vare en Tid i Forvaring.
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 Og de drømte begge en Drøm, hver sin Drøm i een Nat, hver sin Drøm efter sin Udtydning, Kongen af Ægyptens Mundskænk og Bager, som vare Fanger i Fængslets Hus.
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 Og Josef kom til dem om Morgenen og saa dem, og se, de vare bedrøvede.
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 Og han spurgte Faraos Betjente, som vare med ham i Forvaring i hans Herres Hus, og sagde: Hvi se I saa ilde ud i Dag?
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 Og de sagde til ham: Vi drømte en Drøm, og her er ingen, som kan udtyde den. Og Josef sagde til dem: Hører ikke Udtydninger Gud til fortæller mig det dog!
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 Da fortalte den øverste Mundskænk Josef sin Drøm og sagde til ham: Idet jeg drømte, se, da var et Vintræ for mig.
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 Og paa Vintræet vare tre Kviste, og det grønnedes, og dets Blomster fremkom, og Klaserne derpaa fik modne Bær.
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 Og Faraos Bæger var i min Haand, og jeg tog Druerne og trykkede dem i Faraos Bæger og gav Farao Bægeret i Haanden.
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 Da sagde Josef til ham: Denne er Udtydningen derpaa: de tre Vinkviste ere tre Dage.
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 Om tre Dage skal Farao opløfte dit Hoved og sætte dig i dit Sted igen, at du skal give Faraos Bæger i hans Haand, efter den forrige Vis, der du var hans Mundskænk.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Men tænk du paa mig, naar det gaar dig vel, og gør da den Miskundhed mod mig, at du erindrer mig hos Farao, at han tager mig ud af dette Hus.
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 Thi jeg er hemmelig stjaalen af de Hebræers Land; dertil har jeg ikke heller her gjort noget, at de have sat mig i Hulen.
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 Og der den øverste Bager saa, at han havde udtydet det vel, da sagde han til Josef: Jeg drømte ogsaa, og se, der var tre Kurve med Hvedebrød paa mit Hoved.
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 Og i den øverste Kurv var af alle Haande Mad, Bagværk til Farao, og Fuglene aade det af Kurven paa mit Hoved.
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 Da svarede Josef og sagde: Denne er Udtydningen derpaa: de tre Kurve ere tre Dage.
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 Om tre Dage skal Farao opløfte dit Hoved fra dig og hænge dig paa et Træ, og Fuglene skulle æde dit Kød af dig.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 Og det skete paa den tredje Dag, paa Faraos Fødselsdag, da gjorde han alle sine Tjenere et Gæstebud og opløftede den øverste Mundskænks Hoved og den øverste Bagers Hoved iblandt sine Tjenere.
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 Og han satte den øverste Mundskænk til sit Skænkeembede igen, og han rakte Bægeret i Faraos Haand.
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
22 Men den øverste Bager lod han hænge, saasom Josef havde udtydet dem.
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 Og den øverste Mundskænk tænkte ikke paa Josef, men forglemte ham.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.