< 1 Mosebog 36 >
1 Og disse ere Esaus, det er Edoms, Slægter.
Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
2 Esau tog sig Hustruer af Kanaans Døtre: Ada, Elons, den Hethiters Datter, og Oholibama, Anas Datter, Sibeons, den Heviters Datter,
Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
3 og Basmat, Ismaels Datter, Nebajoths Søster.
ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
4 Og Ada fødte Esau Elifas, og Basmat fødte Reguel.
Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
5 Og Oholibama fødte Jeus og Jaelam og Kora; disse ere Esaus Sønner, som fødtes ham i Kanaans Land.
Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
6 Og Esau tog sine Hustruer og sine Sønner og sine Døtre og alle Sjæle i sit Hus og sit Fæ og alt sit Kvæg og alt det Gods, som han havde forhvervet i Kanaans Land og drog til et Land, bort fra sin Broder Jakobs Ansigt.
Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
7 Thi deres Gods var saa meget, at de ikke kunde bo tilsammen; og det Land, hvor de vare fremmede, kunde ikke bære dem for deres Kvægs Skyld.
Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
8 Saa boede Esau paa det Bjerg Sejr; Esau, det er Edom.
Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
9 Og disse ere Esaus, Edomiternes Faders, Slægter, paa det Bjerg Sejr.
Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
10 Disse ere Esaus Sønners Navne: Elifas, Adas, Esaus Hustrus, Søn; Reguel, Basmats, Esaus Hustrus, Søn.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
11 Og disse vare Elifas' Sønner: Theman, Omar, Sefo og Gaetham og Kenas.
’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
12 Og Thimna var Elifas', Esaus Søns, Medhustru, og hun fødte Elifas Amalek; disse ere Adas, Esaus Hustrus, Sønner.
Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
13 Og disse ere Reguels Sønner: Nahath og Serah, Samma og Missa; disse ere Basmats, Esaus Hustrus, Sønner.
’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
14 Og disse vare Sønner af Oholibama, som var Anas Datter, Sibeons Datter, Esaus Hustru; og hun fødte Esau Jeus og Jaelam og Kora.
’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
15 Disse ere Fyrsterne iblandt Esaus Sønner: Elifas', Esaus førstefødtes, Sønner: Fyrsten Theman, Fyrsten Omar, Fyrsten Sefo, Fyrsten Kenas,
Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
16 Fyrsten Kora, Fyrsten Gaetham, Fyrsten Amalek; disse ere Fyrsterne af Elifas i det Land Edom, disse vare Adas Sønner.
Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
17 Og disse ere Reguels, Esaus Søns, Sønner: Fyrsten Nabath, Fyrsten Sera, Fyrsten Samma, Fyrsten Missa; disse ere Fyrsterne af Reguel i Edoms Land; disse ere Basmats, Esaus Hustrus, Sønner.
’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
18 Og disse ere Oholibamas, Esaus Hustrus, Sønner: Fyrsten Jeus, Fyrsten Jaelam, Fyrsten Kora; disse ere Fyrsterne af Oholibama, Anas Datter, Esaus Hustru.
’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
19 Disse ere Esaus Sønner, og disse deres Fyrster; det er Edom.
Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
20 Disse ere Sejrs den Horiters Sønner, som boede i Landet: Lotan og Sobal og Sibeon og Ana
Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
21 og Dison og Ezer og Disan; disse ere Horiternes Fyrster, Sejrs Sønner i det Land Edom.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
22 Og Lotans Sønner vare: Hori og Heman, og Lotans Søster var Thimna.
’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
23 Og disse vare Sobals Sønner: Alvan og Manahath og Ebal, Sefo og Onam.
’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
24 Og disse ere Sibeons Sønner, baade Aja og Ana; denne Ana var det, som fandt varme Kilder i Ørken, der han vogtede sin Fader Sibeons Asener.
’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
25 Og disse vare Anas Børn: Dison, og Oholibama var Anas Datter.
’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
26 Og disse vare Disons Sønner: Hemdan og Esban og Jithran og Keran.
’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
27 Disse vare Ezers Sønner: Bilhan og Savan og Akan.
’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
28 Disse vare Disans Sønner: Uz og Aran.
’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
29 Disse vare Horiternes Fyrster: Fyrsten Lotan, Fyrsten Sobal, Fyrsten Sibeon, Fyrsten Ana,
Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
30 Fyrsten Dison, Fyrsten Ezer, Fyrsten Disan; disse vare Horiternes Fyrster, iblandt deres Fyrster, i Sejrs Land.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
31 Og disse ere de Konger, som regerede i Edoms Land, førend der regerede en Konge over Israels Børn:
Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
32 nemlig Bela, Beors Søn, var Konge i Edom, og hans Stads Navn var Dinhaba.
Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
33 Og Bela døde, og Jobab, Seras Søn fra Bosra, blev Konge i hans Sted.
Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
34 Og Jobab døde, og Husam af Themanitens Land blev Konge i hans Sted.
Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
35 Og Husam døde, og Hadad, Bedads Søn, blev Konge i hans Sted, han, som slog Midianiterne paa Moabs Mark; og hans Stads Navn var Avith.
Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
36 Og Hadad døde, og Samla af Masreka blev Konge i hans Sted.
Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
37 Og Samla døde, og Saul af Rekoboth ved Floden blev Konge i hans Sted.
Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
38 Og Saul døde, og Baal Hanan, Akbors Søn, blev Konge i hans Sted.
Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
39 Og Baal Hanan, Akbors Søn, døde, og Hadar blev Konge i hans Sted, og hans Stads Navn var Pau, og hans Hustrus Navn var Mehetabeel, en Datter af Matred, som var Mesahabs Datter.
Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
40 Og disse vare Fyrsternes Navne, som kom af Esau, efter deres Slægter, i deres Stæder, ved deres Navne: Fyrsten Thimna, Fyrsten Alva, Fyrsten Jetheth,
Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
41 Fyrsten Oholibama, Fyrsten Ela, Fyrsten Pinon,
Oholibama, Ela, Finon.
42 Fyrsten Kenas, Fyrsten Theman, Fyrsten Mibsar,
Kenaz, Teman, Mibzar.
43 Fyrsten Magdiel, Fyrsten Iram; disse ere Fyrsterne i Edom, eftersom de boede i deres eget Land. Denne Esau er Fader til Edomiterne.
Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.