< 1 Mosebog 29 >
1 Og Jakob løftede sine Fødder og gik til det Folks Land i Østen.
Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
2 Og han saa og se, der var en Brønd paa Marken, og se, der vare tre Faarehjorde, som laa ved den; thi man skulde vande Hjorden af den samme Brønd, og Stenen over Hullet paa Brønden var stor.
A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
3 Og derhen skulde alle Hjordene sankes, og Stenen væltes fra Hullet paa Brønden, og Faarene vandes, og Stenen igen lægges over Hullet paa Brønden, paa sit Sted.
Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
4 Og Jakob sagde til dem: Mine Brødre, hvorfra ere I? og de sagde: Fra Karan ere vi.
Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
5 Og han sagde til dem: Kende I Laban, Nakors Søn? og de sagde: Vi kende ham.
Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
6 Og han sagde til dem: Gaar det ham vel? og de sagde: Vel! og se, Rakel, hans Datter, kommer med Faarene.
Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
7 Da sagde han: Se, det er endnu højt paa Dagen, det er ikke Tid, at Kvæget samles; vander Faarene og gaar, vogter dem!
Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
8 Og de sagde: Vi kunne ikke, førend alle Hjordene sankes, og man vælter Stenen fra Hullet paa Brønden, og da vande vi Faarene.
Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
9 Medens han endnu talede med dem, da kom Rakel med Faarene, som vare hendes Faders; thi hun vogtede.
Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
10 Og det skete, der Jakob saa Rakel, sin Morbroder Labans Datter, og Labans, sin Morbroders, Faar, da gik Jakob til og væltede Stenen fra Hullet paa Brønden og vandede Labans, sin Morbroders, Faar.
Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
11 Og Jakob kyssede Rakel og opløftede sin Røst og græd.
Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
12 Og Jakob sagde Rakel, at han var hendes Faders Broder, og at han var Rebekkas Søn; saa løb hun og forkyndte sin Fader det.
Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
13 Og det skete, der Laban hørte den Tidende om Jakob, sin Søstersøn, da løb han mod ham og tog ham i Favn og kyssede ham og ledte ham ind i sit Hus; da fortalte han Laban alle disse Ting.
Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
14 Da sagde Laban til ham: Sandelig, du er mit Ben og mit Kød; og han blev hos ham en Maanedstid.
Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
15 Og Laban sagde til Jakob: Fordi du er min Broder, skulde du derfor tjene mig for intet? sig mig, hvad din Løn skal være.
sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
16 Og Laban havde to Døtre: Den ældstes Navn var Lea, og den yngstes Navn Rakel.
Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
17 Og Lea havde svage Øjne; men Rakel var dejlig af Skikkelse og dejlig af Anseelse.
Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
18 Og Jakob elskede Rakel og sagde: Jeg vil tjene dig syv Aar for Rakel, din yngste Datter.
Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
19 Og Laban sagde: Det er bedre, at jeg giver hende til dig, end at jeg giver hende til en anden Mand, bliv hos mig!
Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
20 Saa tjente Jakob for Rakel syv Aar, og de syntes ham at være faa Dage, fordi han havde Kærlighed til hende.
Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
21 Og Jakob sagde til Laban: Giv mig min Hustru; thi min Tid er fuldkommet, og jeg vil gaa ind til hende.
Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
22 Saa bød Laban alle Mænd paa det Sted tilsammen og gjorde et Gæstebud.
Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
23 Og det skete om Aftenen, at han tog Lea sin Datter og ledte hende ind til ham, og han gik ind til hende.
Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
24 Og Laban gav hende Silpa, sin Tjenestepige, til Pige for Lea, sin Datter.
Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
25 Og det skete om Morgenen, se, da var det Lea; og han sagde til Laban: Hvi gjorde du dette imod mig? har jeg ej tjent hos dig for Rakel? og hvi har du bedraget mig?
Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
26 Og Laban sagde: Det sker ikke saaledes paa vort Sted, at man giver den yngste bort før den førstefødte.
Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
27 Hold dennes Uge ud, saa ville vi ogsaa give dig denne for den Tjeneste, som du skal tjene hos mig endnu syv andre Aar.
Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
28 Og Jakob gjorde saa og holdt dennes Uge ud; saa gav han ham Rakel, sin Datter, til hans Hustru.
Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
29 Og Laban gav sin Datter Rakel Bilha, sin Tjenestepige, til Tjenestepige for hende.
Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
30 Saa gik han og ind til Rakel, og elskede Rakel mere end Lea; og han tjente hos ham endnu syr andre Aar.
Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
31 Der Herren saa, at Lea var foragtet, da aabnede han hendes Moderliv; men Rakel var ufrugtbar.
Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
32 Og Lea undfik og fødte en Søn, og hun kaldte hans Navn Ruben; thi hun sagde: Herren har set paa min Elendighed; thi nu skal min Mand elske mig.
Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
33 Og hun undfik igen og fødte en Søn og sagde: Fordi Herren har hørt, at jeg var forsmaaet, da har han givet mig ogsaa denne; saa kaldte hun hans Navn Simeon.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
34 Og hun undfik igen og fødte en Søn og sagde: Nu denne Sinde skal min Mand holde sig til mig, thi jeg har født ham tre Sønner; derfor kaldte man hans Navn Levi.
Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
35 Og hun undfik igen og fødte en Søn og sagde: Denne Sinde vil jeg prise Herren; derfor kaldte hun hans Navn Juda; saa holdt hun op at føde.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.