< 1 Mosebog 22 >

1 Og det skete derefter, at Gud fristede Abraham og sagde til ham: Abraham! og han sagde: se, her er jeg.
Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
2 Og han sagde: Tag nu din Søn, din eneste, som du har kær, Isak, og gak du til Moria Land og offer ham der til et Brændoffer paa et af Bjergene, som jeg vil sige dig.
Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
3 Saa stod Abraham aarle op om Morgenen og sadlede sit Asen og tog to af sine Drenge med sig og Isak sin Søn; og han kløvede Veddet til Brændofferet og gjorde sig rede og gik til Stedet, som Gud havde sagt ham.
Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
4 Paa den tredje Dag, da opløftede Abraham sine Øjne og saa Stedet langt borte.
A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
5 Da sagde Abraham til sine Drenge: Bliver I her med Asenet, og jeg og Drengen vi ville gaa derhen, og vi ville tilbede og komme til eder igen.
Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
6 Og Abraham tog Veddet til Brændofferet og lagde paa Isak, sin Søn, men han tog Ilden og Kniven i sin Haand, og de gik begge tilsammen.
Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
7 Da talede Isak til Abraham, sin Fader, og sagde: Min Fader! og denne sagde: Se, her er jeg, min Søn; og han sagde: Se, Ilden og Veddet! men hvor er Lammet til Brændofferet?
sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
8 Og Abraham sagde: Gud skal selv udse sig Lammet til Brændofferet, min Søn; saa gik de begge tilsammen.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
9 Og der de kom til det Sted, som Gud havde sagt ham, da byggede Abraham der et Alter og lagde Veddet til Rette, og han bandt Isak, sin Søn, og lagde ham paa Alteret oven paa Veddet.
Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
10 Og Abraham rakte sin Haand ud og greb Kniven for at slagte sin Søn.
Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
11 Da raabte Herrens Engel af Himmelen til ham og sagde: Abraham, Abraham! og han sagde: Se, her er jeg.
Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
12 Og han sagde: Læg ikke din Haand paa Drengen og gør ham intet; thi nu kender jeg, at du frygter Gud og har ikke sparet din Søn, din eneste, for mig.
Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
13 Da opløftede Abraham sine Øjne og saa, og se, en Vædder bag ham var indviklet i Busken ved sine Horn; og Abraham gik og tog Vædderen og ofrede den til Brændoffer i sin Søns Sted.
Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
14 Saa kaldte Abraham det samme Steds Navn: Herren skal se; hvilket siges paa denne Dag: Paa Herrens Bjerg skal ses.
Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
15 Og Herrens Engel raabte til Abraham anden Gang af Himmelen.
Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
16 Og han sagde: Jeg har svoret ved mig, siger Herren, at fordi du gjorde dette og ikke sparede din Søn, den eneste:
ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
17 derfor vil jeg storligen velsigne dig og meget mangfoldiggøre din Sæd som Stjernerne paa Himmelen og som Sand, der er ved Havets Bred, og din Sæd skal eje sine Fjenders Port;
tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
18 og udi din Sæd skulle alle Folk paa Jorden velsignes, fordi du lød min Røst.
ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
19 Saa gik Abraham tilbage til sine Drenge, og de gjorde sig rede og fore tilsammen til Beersaba; thi Abraham boede i Beersaba.
Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
20 Og det skete efter disse Handeler, at det blev Abraham forkyndt, idet man sagde: Se, Milka, hun har ogsaa født din Broder Nakor Sønner,
Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
21 nemlig Uz, hans førstefødte, og Bus, hans Broder, og Kemuel, Arams Fader,
ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
22 og Kesed og Kaso og Pildask og Jidlaf og Bethuel;
Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
23 men Bethuel avlede Rebekka; disse otte fødte Milka Nakor, Abrahams Broder.
Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
24 Og han havde en Medhustru, og hendes Navn var Reuma, og hun fødte ogsaa Tebak og Gakam og Takask og Maaka.
Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.

< 1 Mosebog 22 >