< Galaterne 4 >
1 Men jeg siger: Saa længe Arvingen er umyndig, er der ingen Forskel imellem ham og en Træl, skønt han er Herre over alt Godset;
Abin da nake nufi shi ne, muddin magāji yana ɗan yaro ne tukuna, babu bambanci tsakaninsa da bawa, ko da yake shi ne da mallakar kome.
2 men han staar under Formyndere og Husholdere indtil den af Faderen bestemte Tid.
Yana ƙarƙashin iyayen goyonsa da masu riƙon amana har yă zuwa cikar lokacin da mahaifinsa ya sa.
3 Saaledes stode ogsaa vi, dengang vi vare umyndige, som Trælle under Verdens Børnelærdom.
Haka yake, sa’ad da muke’yan yara, mun kasance cikin bauta a ƙarƙashin ƙa’idodin duniya.
4 Men da Tidens Fylde kom, udsendte Gud sin Søn, født af en Kvinde, født under Loven,
Amma da lokacin da aka tsara ya yi sosai, sai Allah ya aiki Ɗansa, haifaffe daga mace, haifaffe a ƙarƙashin Doka,
5 for at han skulde løskøbe dem, som vare under Loven, for at vi skulde faa Sønneudkaarelsen.
domin yă fanshi waɗanda suke a ƙarƙashin doka, saboda mu sami cikakken matsayin zaman’ya’ya.
6 Men fordi I ere Sønner, har Gud udsendt i vore Hjerter sin Søns Aand, som raaber: Abba, Fader!
Da yake ku’ya’ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, Ruhun da yake kira, “Abba, Uba.”
7 Altsaa er du ikke længer Træl, men Søn; men er du Søn, da er du ogsaa Arving ved Gud.
Saboda haka kai ba bawa ba ne kuma, kai ɗa ne; da yake kuwa kai ɗa ne, Allah ya mai da kai magāji.
8 Dengang derimod, da I ikke kendte Gud, trællede I for de Guder, som af Natur ikke ere det.
Dā da ba ku san Allah ba, ku bayi ne ga waɗanda a ainihi ba alloli ba ne.
9 Men nu, da I have lært Gud at kende, ja, meget mere ere blevne kendte af Gud, hvor kunne I da atter vende tilbage til den svage og fattige Børnelærdom, som I atter forfra ville trælle under?
Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma a ce Allah ya san ku, yaya kuke sāke komawa ga ƙa’idodin duniya marasa ƙarfi, abin tausayi kuma? Kuna so ku sāke komawa ga bautarsu ne?
10 I tage Vare paa Dage og Maaneder og Tider og Aar.
Kuna kiyaye ranaku da watanni da lokuta da shekaru na musamman!
11 Jeg frygter for, at jeg maaske har arbejdet forgæves paa eder.
Kai, kun ba ni tsoro, don ya zama kamar duk wahalar da na yi a kanku banza ne!
12 Vorder ligesom jeg, thi ogsaa jeg er bleven som I, Brødre! jeg beder eder. I have ikke gjort mig nogen Uret.
Ina roƙonku’yan’uwa, ku zama kamar ni, gama na zama kamar ku. Ba ku yi mini wani laifi ba.
13 Men I vide, at det var paa Grund af en Kødets Svaghed, at jeg første Gang forkyndte Evangeliet for eder;
Kun san rashin lafiyar da na yi, shi ne ya yi mini hanyar da na kawo muku bishara da farko.
14 og det, som i mit Kød var eder til Fristelse, ringeagtede I ikke og afskyede I ikke, men I modtoge mig som en Guds Engel, som Kristus Jesus.
Ko da yake ciwona gwaji ne gare ku, ba ku yi mini reni ko ƙyama ba. A maimakon haka, kuka karɓe ni sai ka ce mala’ikan Allah, kuma sai ka ce Kiristi Yesu kansa.
15 Hvor er da nu eders Saligprisning? Thi jeg giver eder det Vidnesbyrd, at, om det havde været muligt, havde I udrevet eders Øjne og givet mig dem.
Me ya faru da dukan farin cikinku? Na tabbata, a lokacin, da mai yiwuwa ne da kun ciccire idanunku kun ba ni.
16 Saa er jeg vel bleven eders Fjende ved at tale Sandhed til eder?
Yanzu na zama abokin gābanku don na faɗa muku gaskiya ke nan?
17 De ere nidkære for eder, dog ikke for det gode; men de ville udelukke eder, for at I skulle være nidkære for dem.
Waɗancan mutane suna neman su rinjaye ku da ƙwazo, amma ba da kyakkyawar aniya ba. Abin da suke so shi ne su raba ku da mu, saboda ƙwazonku yă koma gare su.
18 Men det er godt at vise sig nidkær i det gode til enhver Tid, og ikke alene, naar jeg er nærværende hos eder.
Yana da kyau ku kasance da irin wannan niyya idan da nufi mai kyau ne, ku kuma kasance a haka koyaushe ba sai ina tare da ku ba.
19 Mine Børn, som jeg atter føder med Smerte, indtil Kristus har vundet Skikkelse i eder!
Ya ku’ya’yana ƙaunatattu, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har sai Kiristi ya kahu a cikinku.
20 — ja jeg vilde ønske, at jeg nu var til Stede hos eder og kunde omskifte min Røst; thi jeg er raadvild over for eder.
Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canja muryata mana! Gama na damu ƙwarai saboda ku!
21 Siger mig, I, som ville være under Loven, høre I ikke Loven?
Ku gaya mini, ku da kuke so ku zauna a ƙarƙashin Doka, ba ku san abin da Doka ta ce ba ne?
22 Der er jo skrevet, at Abraham havde to Sønner, en med Tjenestekvinden og en med den frie Kvinde.
Gama a rubuce yake cewa Ibrahim yana da’ya’ya biyu maza, ɗaya ta wurin mace’yar aikin gidansa, ɗaya kuma ta wurin ainihin matarsa.
23 Men Tjenestekvindens Søn er avlet efter Kødet, den frie Kvindes ved Forjættelsen.
Ɗansa na wajen mace’yar aikin gidansa ya zo bisa ga ƙa’idar jiki ne; amma ɗansa na wajen ainihin matarsa ya zo a sakamakon alkawarin ne.
24 Dette har en billedlig Betydning. Thi disse Kvinder ere tvende Pagter, den ene fra Sinai Bjerg, som føder til Trældom: Denne er Hagar.
Za a iya ɗaukan waɗannan al’amura a matsayin misali, domin matan nan suna misalta alkawura biyu ne. Alkawari ɗaya daga Dutsen Sinai ne yana kuma haihuwar’ya’yan da za su zama bayi. Hagar ke nan.
25 Thi „Hagar” er Sinai Bjerg i Arabien, men svarer til det nuværende Jerusalem; thi det er i Trældom med sine Børn.
Hagar tana a matsayin Dutsen Sinai a Arabiya tana kuma kwatancin birnin Urushalima na yanzu, gama ita baiwa ce tare da’ya’yanta.
26 Men Jerusalem heroventil er frit, og hun er vor Moder.
Amma Urushalimar da take sama’yantacciya ce, ita ce kuma mahaifiyarmu.
27 Thi der er skrevet: „Fryd dig, du ufrugtbare, du, som ikke føder! bryd ud og raab, du, som ikke har Fødselsveer! thi mange ere den enliges Børn fremfor hendes, som har Manden.”
Gama a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakararriya, wadda ba ta haihuwa ki ɓarke da murna, ki kuma tā da murya, ke da ba kya naƙuda; domin da yawa ne’ya’yan macen da aka yashe, fiye da na mai miji.”
28 Men vi, Brødre! ere Forjættelsens Børn i Lighed med Isak.
To, ku’yan’uwa, ku’ya’yan alkawari ne kamar Ishaku.
29 Men ligesom dengang han, som var avlet efter Kødet, forfulgte ham, som var avlet efter Aanden, saaledes ogsaa nu.
A wancan lokaci, wannan ɗa wanda aka haifa ta wurin ƙa’idar jiki ya tsananta wa wanda aka haifa ta ikon Ruhu. Haka ma yake har yanzu.
30 Men hvad siger Skriften: „Uddriv Tjenestekvinden og hendes Søn; thi Tjenestekvindens Søn skal ingenlunde arve med den frie Kvindes Søn.”
Amma me Nassi ya ce? Nassi ya ce, “Kori macen nan’yar aikin gida da ɗanta don ɗan mace’yar aikin gida ba zai taɓa raba gādo tare da ɗa na ainihin matarka ba.”
31 Derfor, Brødre! ere vi ikke Tjenestekvindens Børn, men den frie Kvindes.
Saboda haka,’yan’uwa, mu ba’ya’yan mace’yar aikin gida ba ne, amma na ainihin matan gidan ne.