< Ezekiel 39 >

1 Og du Menneskesøn! spaa imod Gog, og sig: Saa siger den Herre, Herre: Se, jeg kommer imod dig, Gog, du Fyrste over Rosk, Mesek og Tubal.
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
2 Og jeg vil vende dig om og drive dig frem og føre dig op fra det yderste Nord og lade dig komme over Israels Bjerge.
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
3 Og jeg vil slaa din Bue ud af din venstre Haand og lade dine Pile falde ud af din højre Haand.
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
4 Paa Israels Bjerge skal du falde, du og alle dine Hære og de Folk, som ere med dig; jeg vil give dig til Føde for Rovfuglene, Smaafuglene, alt det bevingede og de vilde Dyr paa Marken.
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
5 Paa den vide Mark skal du falde; thi jeg har talt det, siger den Herre, Herre.
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 Og jeg vil sende en Ild paa Magog og paa dem, som bo tryggelig Paa Øerne, og de skulle fornemme, at jeg er Herren.
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
7 Og jeg vil kundgøre mit hellige Navn midt iblandt mit Folk Israel og ikke ydermere lade mit hellige Navn vanhelliges, og Hedningerne skulle fornemme, at jeg er Herren, den Hellige i Israel.
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
8 Se, det kommer, og det skal ske, siger den Herre, Herre; det er den Dag, som jeg har talt om.
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
9 Og Indbyggerne i Israels Stæder skulle gaa ud og gøre Ild paa og hede med Rustninger og smaa Skjolde og store Skjolde, med Bue og med Pile og med Haandstav og med Spyd, og de skulle gøre Ild dermed i syv Aar.
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
10 Og de skulle ikke hente Træ fra Marken eller hugge af Skovene; thi de skulle gøre Ild med Rustninger; og de skulle røve fra dem, for hvilke de vare et Rov, og plyndre dem, af hvilke de bleve plyndrede, siger den Herre, Herre.
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
11 Og det skal ske paa denne Dag, at jeg vil give Gog et Sted der til Begravelse i Israel, de vejfarendes Dal Østen for Havet, og den skal bringe de vejfarende til at holde sig for Næsen; og der skulle de begrave Gog og al hans Mangfoldighed og kalde den Gogs Mangfoldigheds Dal.
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
12 Og Israels Hus skal begrave dem, for at rense Landet, i syv Maaneder;
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
13 ja, alt Folket i Landet skal begrave dem, og det skal vorde dem til et Navn, paa den Dag, jeg forherliger mig, siger den Herre, Herre.
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
14 Og de skulle udnævne faste Mænd, nogle, som skulle gaa igennem Landene, og nogle, som tillige med dem, der gaa igennem Landet, skulle begrave dem, der maatte være blevne tilbage oven paa Jorden, for at rense det; naar syv Maaneder ere til Ende, skulle de gennemsøge det.
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
15 Og de, som gaa igennem Landene, skulle gaa omkring, og naar nogen ser et Menneskes Ben, da skal han sætte et Mærke derved, indtil de, som begrave, begrave det i Gogs Mangfoldigheds Dal.
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
16 Og der skal ogsaa en Stad kaldes Hamona; saa skulle de rense Landet.
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
17 Og du Menneskesøn! saa siger den Herre, Herre: Sig til Fuglene, alt det bevingede, og til alle vilde Dyr paa Marken: Samler eder og kommer, sanker eder trindt omkring fra til mit Slagtoffer, som jeg slagter for eder, et stort Slagtoffer paa Israels Bjerge, og I skulle æde Kød og drikke Blod.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
18 I skulle æde de vældiges Kød og drikke Jordens Fyrsters Blod: Vædres, Lams og Bukkes, Øksnes, som alle ere fedede i Basan.
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
19 Og I skulle æde det fede, til I blive mætte, og drikke Blod, til I blive drukne, af mit Slagtoffer, som jeg slagter til eder.
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
20 Og I skulle mætte eder ved mit Bord af Heste og Rytteri, at de vældige og alle Haande Krigsmænd, siger den Herre, Herre.
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 Og jeg vil vise min Herlighed iblandt Hedningerne, og alle Hedningerne skulle se min Dom, som jeg har holdt, og min Haand, som jeg har lagt paa dem.
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
22 Og Israels Hus skal fornemme, at jeg er Herren deres Gud, fra den samme Dag af og fremdeles.
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
23 Og Hedningerne skulle kende, at Israels Hus blev bortført for deres Misgerning, fordi de havde været troløse imod mig, saa at jeg skjulte mit Ansigt for dem og gav dem i deres Fjenders Haand, og de alle faldt for Sværdet.
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
24 Efter deres Urenhed og efter deres Overtrædelser handlede jeg imod dem, og jeg skjulte mit Ansigt for dem.
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
25 Derfor, saa siger den Herre, Herre: Nu vil jeg vende Jakobs Fangenskab og forbarme mig over Israels hele Hus og være nidkær for mit hellige Navn.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
26 Og de skulle bære deres Skam og al Jeres Troløshed, som de begik imod mig, naar de bo tryggelig i deres Land, og der ingen er, som forfærder dem,
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
27 naar jeg fører dem tilbage fra Folkene og sanker dem fra deres Fjenders Lande, og naar jeg helliggør mig paa dem for mange Hedningers Øjne.
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
28 Og de skulle fornemme, at jeg er Herren deres Gud, idet jeg har bortført dem til Hedningerne og nu samler dem til deres Land og ikke ydermere lader nogen af dem blive tilbage hist.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
29 Jeg vil og ikke mere skjule mit Ansigt for dem; thi jeg har udgydt min Aand over Israels Hus, siger den Herre, Herre.
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 39 >