< Ezekiel 25 >

1 Og Herrens Ord kom til mig saaledes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Du Menneskesøn! vend dit Ansigt imod Ammons Børn, og spaa imod dem,
“Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
3 og sig til Ammons Børn: Hører den Herre, Herres Ord: Saa siger den Herre, Herre: Efterdi du sagde: Ha ha! over min Helligdom, fordi den er vanhelliget, og over Israels Land, fordi det er ødelagt, og over Judas Hus, fordi de ere vandrede i Landflygtighed:
Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
4 Derfor se, jeg vil give dig til Ejendom for Østens Folk, og de skulle opslaa deres Teltbyer i dig og sætte deres Boliger i dig; de skulle æde din Frugt, og de skulle drikke din Mælk.
saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
5 Og jeg vil gøre Rabba til Græsgang for Kameler og Ammons Børns Land til Faareleje; og I skulle fornemme, at jeg er Herren.
Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
6 Thi saa siger den Herre, Herre: Fordi du klappede i Haanden og stampede med Foden og glædede dig i al din Haan efter din Sjæls Lyst imod Israels Land:
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
7 Derfor se, jeg ud rækker min Haand imod dig og giver dig hen til Bytte for Folkene og udrydder dig af Folkeslægternes Tal og lader dig forsvinde af Lan dene; jeg vil ødelægge dig, og du skal fornemme, at jeg er Herren.
saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
8 Saa siger den Herre, Herre: Fordi Moab og Sejr sige: Se, Judas Hus er ligesom alle Hedningerne:
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
9 Derfor se, jeg vil aabne Moabs Side fra Stæderne af, fra dets Grænsestæder af, Landets Pryd, Beth-Jesimoth, Baal-Meon og Kirjathama,
saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
10 for Østens Børn tillige med Ammons Børns Land, og jeg vil give dem det til Ejendom, paa det man ikke skal ihukomme Ammons Børn iblandt Folkene;
Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
11 og jeg vil holde Ret over Moab, at de skulle fornemme, at jeg er Herren.
zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
12 Saa siger den Herre, Herre: Fordi Edom tog en svar Hævn over Judas Hus og gjorde sig saare skyldig, da de hævnede sig paa dem:
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
13 Derfor, saa siger den Herre, Herre: Jeg vil udrække min Haand over Edom og udrydde Mennesker og Kvæg deraf: Og jeg vil gøre det øde fra Theman af, og indtil Dedan skulle de falde ved Sværdet;
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
14 og jeg vil føre min Hævn over Edom ved mit Folk Israels Haand, og de skulle gøre ved Edom efter min Vrede og efter min Fortørnelse, og de skulle kende min Hævn, siger den Herre, Herre.
Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 Saa siger den Herre, Herre: Fordi Filisterne have taget Hævn og have hævnet sig svarlig i Haan efter deres Sjæls Lyst for at ødelægge med et evigt Fjendskab:
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
16 Derfor, saa siger den Herre, Herre: Se, jeg vil udrække min Haand over Filisterne og udrydde Kreterne; og jeg vil tilintetgøre de overblevne ved Havets Strand;
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
17 og jeg vil tage en stor Hævn over dem med grumme Straffe, og de skulle fornemme, at jeg er Herren, naar jeg fører min Hævn over dem.
Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”

< Ezekiel 25 >