< Ezekiel 14 >
1 Og der kom Mænd af Israels Ældste til mig og sade for mit Ansigt.
Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
2 Og Herrens Ord kom til mig saaledes:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
3 Du Menneskesøn! disse Mænd have givet deres Afguder Plads i deres Hjerte, og hvad der var dem Anstød til at synde, have de stillet for deres Ansigt; skulde jeg vel lade mig adspørge for dem?
“Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
4 Derfor tal med dem, og sig til dem: Saa siger den Herre, Herre: Enhver Mand af Israels Hus, som giver sine Afguder Plads i sit Hjerte og stiller, hvad der var ham Anstød til at synde, for sit Ansigt og saa kommer til Profeten: For ham vil jeg, Herren, lade mig bringe til at svare desangaaende, nemlig angaaende hans Afguders Mangfoldighed,
Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
5 for at jeg kan gribe Israels Hus ved deres Hjerte, fordi de vege fra mig alle sammen ved deres Afguder.
Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
6 Derfor sig til Israels Hus: Saa siger den Herre, Herre: Omvender eder, og vender eder bort fra eders Afguder, ja, vender eders Ansigter bort fra alle eders Vederstyggeligheder!
“Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
7 Thi naar en Mand af Israels Hus eller af de fremmede, som opholde sig i Israel, skiller sig fra mig og giver sine Afguder Plads i sit Hjerte og stiller, hvad der var ham Anstød til at synde, for sit Ansigt og saa kommer til Profeten for at adspørge mig for sig: Ham vil jeg, Herren, lade mig bringe til at give et Svar fra mig selv.
“‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
8 Og jeg vil rette mit Ansigt imod denne Mand og ødelægge ham, at han bliver til et Tegn og til et Ordsprog, og jeg vil udrydde ham af mit Folks Midte; og I skulle fornemme, at jeg er Herren.
Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
9 Men naar Profeten lader sig overtale og taler noget, da har jeg, Herren, ladet denne Profet overtales; og jeg vil udrække min Haand over ham og ødelægge ham ud af mit Folk Israels Midte.
“‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
10 Og de skulle bære deres Misgerning; som hans Misgerning er, der adspørger, saa skal Profetens Misgerning være,
Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
11 for at de af Israels Hus ikke mere skulle fare vild fra mig ej heller besmitte sig mere med nogen af deres Overtrædelser; men de skulle være mit Folk, og jeg skal være deres Gud, siger den Herre, Herre.
Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
12 Og Herrens Ord kom til mig saaledes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
13 Du Menneskesøn! naar et Land synder imod mig, saa at det bliver troløst imod mig, og jeg udrækker min Haand over det og formindsker Brøds Forraad for det, og jeg sender Hunger i det og udrydder Menneske og Fæ deraf,
“Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
14 men der var disse tre Mænd, Noa, Daniel Og Job derudi: Da skulde disse alene redde deres Sjæl ved deres Retfærdighed, siger den Herre, Herre.
ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Naatr jeg lader vilde Dyr gaa igennem Landet, og de berøve Folk deres Børn, og det blev øde, saa at ingen gaar der igennem for Dyrenes Skyld,
“Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
16 men hine tre Mænd vare derudi, saa sandt jeg lever, siger den Herre, Herre: De skulde hverken redde Sønner eller Døtre; de selv alene skulde reddes, men Landet vorde øde.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
17 Eller naar jeg lader Sværdet komme over det samme Land, og jeg siger: Sværd! du skal fare igennem Landet, og jeg udrydder Menneske og Fæ deraf,
“Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
18 men hine tre Mænd vare derudi, saa sandt jeg lever, siger den Herre, Herre: De skulde ikke redde Sønner eller Døtre; men de alene skulde reddes.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
19 Eller naar jeg sender Pest i det samme Land og udøser min Harme over det med Blod, saa at jeg udrydder Menneske og Fæ deraf,
“Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
20 men Noa, Daniel og Job vare derudi, saa sandt jeg lever, siger den Herre, Herre: De skulde hverken redde Søn eller Datter; men de skulde redde deres egen Sjæl ved deres Retfærdighed.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
21 Thi saa siger den Herre, Herre: Meget mere, naar jeg sender mine fire grumme Straffedomme over Jerusalem, nemlig: Sværd og Hunger og vilde Dyr og Pest for at udrydde Menneske og Fæ deraf,
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
22 og se, der bliver nogle undkomne tilovers, som bortføres, Sønner og Døtre: Se, de skulle gaa ud til eder, og I skulle se deres Vej og deres Gerninger; og I skulle trøste eder over den Ulykke, som jeg lod komme over Jerusalem, ja, alt det, som jeg lod komme over den.
Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
23 Og de skulle trøste eder, naar I se deres Vej og deres Gerninger; og I skulle erkende, at jeg intet har gjort uden Grund af alt det, som jeg gjorde derudi, siger den Herre, Herre.
Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”