< 2 Mosebog 8 >
1 Og Herren sagde til Mose: Gak til Farao, og du skal sige til ham: Saa siger Herren: Lad mit Folk fare, at de kunne tjene mig.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
2 Og dersom du vægrer dig ved at lade dem fare, se, da vil jeg plage hele dit Landemærke med Frøer.
In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
3 Og Floden skal vrimle med Frøer, og de skulle hoppe op og komme i dit Hus og i dit Sengekammer og paa din Seng og i dine Tjeneres Hus og iblandt dit Folk og i dine Ovne og i dine Dejgtruge.
Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
4 Og Frøerne skulle hoppe op paa dig og paa dit Folk og paa alle dine Tjenere.
Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
5 Og Herren sagde til Mose: Sig til Aron: Ræk din Haand ud med din Stav over Strømmene, over Floderne og over Søerne, og lad Frøerne komme op over Ægyptens Land.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
6 Og Aron rakte sin Haand ud over Vandene i Ægypten, og der kom Frøer op og skjulte Ægyptens Land.
Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
7 Og Koglerne gjorde ligesaa med deres Besværgelser, og de lode Frøer komme op over Ægyptens Land.
Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
8 Da kaldte Farao ad Mose og Aron og sagde: Beder til Herren, at han borttager Frøerne fra mig og fra mit Folk, saa vil jeg lade Folket fare, og de maa ofre til Herren.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
9 Og Mose sagde til Farao: Hav du fremfor mig den Ære at sige, naar jeg skal bede for dig og for dine Tjenere og for dit Folk, at Frøerne skulle fordrives fra dig og fra dine Huse; kun i Floden skulle de blive tilbage.
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
10 Og han sagde: I Morgen; og han sagde: Efter dit Ord! at du skal fornemme, at der er ikke nogen som Herren vor Gud,
Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
11 saa skulle Frøerne vige fra dig og fra dine Huse og fra dine Tjenere, og fra dit Folk; kun i Floden skulle de blive tilbage.
Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
12 Saa gik Mose og Aron ud fra Farao; og Mose raabte til Herren angaaende de Frøer, som han havde paaført Farao.
Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
13 Og Herren gjorde efter Mose Ord; saa døde Frøerne bort af Husene, af Gaardene og af Agrene.
Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
14 Og de samlede dem sammen, Hob ved Hob, og Landet stinkede.
Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
15 Der Farao saa, at han havde faaet Luft, da forhærdede han sit Hjerte, og han hørte dem ikke, som Herren havde sagt.
Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
16 Og Herren sagde til Mose: Sig til Aron: Ræk din Stav ud, og slaa Støvet paa Jorden; det skal blive til Lus i hele Ægyptens Land.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
17 Og de gjorde saa; og Aron udstrakte sin Haand med sin Stav og slog Støvet paa Jorden, og der blev Lus paa Mennesker og paa Kvæget; alt Støvet i Landet blev til Lus i hele Ægyptens Land.
Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
18 Og Koglerne gjorde ligesaa med deres Besværgelser for at lade Lus komme frem, men de kunde ikke; og der var Lus paa Menneskene og paa Kvæget.
Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
19 Da sagde Koglerne til Farao: Det er Guds Finger; men Faraos Hjerte forhærdedes, saa at han ikke hørte dem, som Herren havde sagt.
Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
20 Og Herren sagde til Mose: Staa aarle op om Morgenen, og stil dig for Farao; se, han gaar ud til Vandet, og du skal sige til ham: Saa siger Herren: Lad mit Folk fare, at de maa tjene mig.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
21 Thi dersom du ikke lader mit Folk fare, se, da lader jeg komme alle Haande Utøj paa dig og paa dine Tjenere og paa dit Folk og i dine Huse, at Ægypternes Huse skulle vorde fulde af allehaande Utøj, og tilmed Jorden, hvorpaa de ere.
In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
22 Og paa den samme Dag vil jeg udskille Gosen Land, i hvilket mit Folk er, at der ikke skal være alle Haande Utøj der, paa det du skal fornemme, at jeg er Herren midt i Landet.
“‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
23 Og jeg vil sætte en Frelse til at skille imellem mit Folk og imellem dit Folk; i Morgen skal det Tegn ske.
Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
24 Og Herren gjorde saa; og der kom en svær Hob Utøj i Faraos Hus og i hans Tjeneres Hus, og i hele Ægyptens Land blev Landet fordærvet af alle Haande Utøj.
Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
25 Og Farao kaldte ad Mose og ad Aron og sagde: Gaar hen, ofrer til eders Gud i dette Land.
Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
26 Og Mose sagde: Det maa ikke ske, at vi saa gøre; thi vi skulde da ofre til Herren vor Gud, Ægypterne til en Vederstyggelighed; se, skulle vi ofre, Ægypterne til en Vederstyggelighed for deres Øjne, og de skulde ikke stene os?
Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
27 Vi skulle gaa tre Dages Rejse i Ørken og ofre til Herren vor Gud, saasom han skal sige os.
Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
28 Da sagde Farao: Jeg vil lade eder fare, at I skulle ofre til Herren eders Gud i Ørken, dog saa, at I ikke skulle drage længere bort; beder for mig.
Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
29 Og Mose sagde: Se, naar jeg kommer ud fra dig, da vil jeg bede til Herren, at alle Haande Utøj skal vige fra Farao og fra hans Tjenere og fra hans Folk i Morgen; kun at Farao ikke bedrager mig mere, saa at han ej lader Folket fare at ofre til Herren.
Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
30 Og Mose gik ud fra Farao og bad til Herren.
Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
31 Saa gjorde Herren efter Mose Ord og borttog alle Haande Utøj fra Farao, fra hans Tjenere og fra hans Folk; der blev ikke eet igen.
Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
32 Men Farao forhærdede sit Hjerte end denne Gang og lod ikke Folket fare.
Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.