< 2 Mosebog 22 >

1 Naar nogen stjæler en Okse eller et Lam og slagter det eller sælger det, skal han betale fem Okser for Oksen og fire Lam for Lammet.
“In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
2 Om nogen Tyv bliver greben, idet han bryder ind, og bliver slagen og dør, skal ingen Bloddom udgaa for hans Skyld.
“In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
3 Men er Solen opgangen over ham, da skal Bloddom udgaa for hans Skyld. Tyven skal betale; men har han intet, da skal han sælges for sit Tyveri.
amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
4 Dersom det stjaalne findes i hans Vold, hvad enten det er Okse eller Asen eller Lam, som er levende, skal han betale dobbelt.
In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
5 Naar nogen lader afæde Ager eller Vingaard, idet han slaar sit Kvæg løs, og det afæder en andens Ager, da skal han betale af det bedste paa sin Ager og af det bedste i sin Vingaard.
“In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
6 Om Ild farer ud og griber fat i Torne, og Negene eller det staaende Korn eller Ageren ødelægges, da skal han, som antændte Branden, visselig betale.
“In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
7 Om nogen flyr sin Næste Penge eller Tøj at forvare, og det bliver stjaalet af Mandens Hus, skal Tyven, hvis han findes, betale dobbelt.
“In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
8 Men findes Tyven ikke, da skal Husbonden føres frem for Gud at vidne, at han ikke har lagt sin Haand paa sin Næstes Tøj.
Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
9 Hvad angaar al svigagtig Handel, om Okse, Asen, Lam, Klæder, om alt, hvad der er tabt, om hvilket nogen siger, at dette er hans, da skal begges Sag komme for Gud; hvem Gud siger at være skyldig, han skal betale sin Næste dobbelt.
A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
10 Naar nogen flyr sin Næste Asen eller Okse eller Lam eller andet Kvæg at passe paa, og det dør, eller det kommer til Skade, eller det bortføres, og ingen ser det,
“In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
11 da skal Ed ved Herren være imellem dem begge, at han ikke har lagt sin Haand paa sin Næstes Gods, og den skal dets Ejermand tage for god, og den anden skal ikke betale.
rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
12 Men bliver det stjaalet fra ham, da skal han betale dets Ejermand det.
Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
13 Men bliver det sønderrevet, da skal han føre det frem til et Vidnesbyrd; han skal ikke betale det, som er sønderrevet.
In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
14 Og naar nogen laaner noget af sin Næste, og det kommer til Skade eller dør, da skal han, hvis Ejermanden ikke er til Stede, betale det.
“In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
15 Dersom dets Ejermand er derhos, da skal han ikke betale; dersom det er lejet, da regnes det for Lejen.
Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
16 Og naar nogen lokker en Jomfru, som ikke er trolovet, og ligger hos hende, da skal han visselig give Morgengave for hende og tage sig hende til Hustru.
“Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
17 Men om hendes Fader vægrer sig ved at give ham hende, da skal han tilveje Penge efter Morgengave for en Jomfru.
In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
18 Du skal ikke lade en Troldkvinde leve.
“Kada ku bar maiya da rai.
19 Hver som ligger hos et Dyr, skal visselig dødes.
“Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
20 Hvo som ofrer til Guderne og ikke til Herren alene, skal være forbandet.
“Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
21 Og du skal ikke plage en fremmed og ikke undertrykke ham; thi I have været fremmede i Ægyptens Land.
“Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
22 I skulle ikke plage nogen Enke eller faderløs.
“Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
23 Dersom du plager ham, og han raaber til mig, da skal jeg visselig høre hans Raab.
In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
24 Saa optændes min Vrede, og jeg ihjelslaar eder med Sværd, og eders Hustruer skulle blive Enker og eders Børn faderløse.
Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
25 Dersom du laaner mit Folk Penge, nemlig den fattige hos dig, da skal du ikke være ham som en Aagerkarl; I skulle ikke lægge Aager paa ham.
“In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
26 Dersom du tager din Næstes Klædebon til Pant, da skal du give ham det igen, førend Solen gaar ned.
In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
27 Thi det er hans eneste Skjul, det er hans Klædebon for hans Krop; deri ligger han; og det skal ske, naar han raaber til mig, da skal jeg høre det, thi jeg er naadig.
domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
28 Du skal ikke bande Gud, og den øverste iblandt dit Folk skal du ikke ønske ondt over.
“Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
29 Du skal ikke tøve med at give mig af din Lades Fylde og din Vinperses Væde; du skal give mig den førstefødte af dine Sønner.
“Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
30 Saaledes skal du gøre med din Okse og med dit Faar; det skal være syv Dage hos sin Moder, paa den ottende Dag skal du give mig det.
Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
31 Og I skulle være mig aldeles hellige Mennesker og ikke æde Kød, som er sønderrevet paa Marken; for Hunde skulle I kaste det.
“Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.

< 2 Mosebog 22 >