< 2 Mosebog 16 >
1 Og de droge fra Elim, og al Israels Børns Menighed kom til den Ørk Sin, som er imellem Elim og imellem Sinai, paa den femtende Dag i den anden Maaned, efter at de udgik af Ægyptens Land.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 Og al Israels Børns Menighed knurrede mod Mose og mod Aron i Ørken.
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 Og Israels Børn sagde til dem: Gid vi vare døde ved Herrens Haand i Ægyptens Land, da vi sade ved Kødgryden, da vi aade Brød, til vi vare mætte; thi I have udført os i denne Ørk at lade hele denne Menighed dø af Hunger.
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 Da sagde Herren til Mose: Se, jeg vil lade regne Brød ned fra Himmelen til eder, at Folket maa gaa ud og sanke, hvad der hører til, Dag for Dag, at jeg kan forsøge det, om det vil vandre i min Lov eller ej.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 Og det skal ske paa den sjette Dag, at de skulle tillave det, som de bære hjem; og det skal være dobbelt saa meget som det, de ellers sanke hver Dag.
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 Og Mose og Aron sagde til alle Israels Børn: I Aften skulle I kende, at Herren har udført eder af Ægyptens Land;
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 og i Morgen skulle I se Herrens Herlighed, efterdi han har hørt eders Knurren imod Herren; og hvad ere vi, at I knurre mod os?
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 Og Mose sagde: Det skal ske, naar Herren giver eder Kød at æde i Aften og Brød i Morgen til at mættes; efterdi Herren har hørt eders Knurren, med hvilken I knurre imod ham; og hvad ere vi? Eders Knurren er ikke imod os, men imod Herren.
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 Og Mose sagde til Aron: Sig til al Israels Børns Menighed: Kommer frem for Herrens Ansigt; thi han har hørt eders Knurren.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 Og det skete, der Aron talede til al Israels Børns Menighed, da saa de hen til Ørken; og se, Herrens Herlighed saas i Skyen.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 Og Herren talede til Mose og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 Jeg har hørt Israels Børns Knurren; tal til dem og sig: Imellem de to Aftener skulle I æde Kød, og i Morgen skulle I mættes af Brød; og I skulle fornemme, at jeg er Herren eders Gud.
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 Og det skete om Aftenen, at der kom Vagtler og bedækkede Lejren, og om Morgenen laa Duggen trindt omkring Lejren.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 Og der Duggen, som laa, hævede sig, se, da laa der oven over Ørken noget tyndt, trindt, tyndt som Rimfrost paa Jorden.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 Der Israels Børn saa det, da sagde de, den ene til den anden: Hvad er det? thi de vidste ikke, hvad det var; da sagde Mose til dem: Det er det Brød, som Herren har givet eder at æde.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 Dette er det Ord, som Herren har befalet: Sanker deraf, eftersom enhver kan æde; I skulle tage en Orner for hvert Hoved, efter eders Personers Tal, som hver har i sit Telt.
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 Og Israels Børn gjorde saa og sankede, en mere og en anden mindre.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 Og de maalte det i en Orner, da havde den ikke tilovers, som havde sanket meget, og der fattedes ikke for den, som havde sanket mindre; de havde sanket hver saa meget, som han kunde æde.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 Og Mose sagde til dem: Ingen skal levne deraf til om Morgenen.
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 Dog adløde de ikke Mose, men somme levnede deraf til om Morgenen, saa voksede der Orme derudi, og det lugtede ilde; saa blev Mose vred paa dem.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 Og de sankede hver Morgen deraf, hver saa meget, som han kunde æde, men naar Solen skinnede hedt, saa smeltedes det.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 Og det skete paa den sjette Dag, at de sankede dobbelt Brød, to Orner for een; saa kom alle Fyrsterne af Menigheden og gav Mose det til Kende.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 Da sagde han til dem: Det er det, som Herren sagde: I Morgen er det Sabbat, Helligheds Hvile for Herren; hvad I ville bage, det bager, og hvad I ville koge, det koger; men alt det, som bliver tilovers, skulle I lade ligge i Forvaring for eder til Morgenen.
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 Og de lode det ligge til Morgenen, som Mose befalede; og det lugtede ikke ilde, og der var ikke Orm i det.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 Da sagde Mose: Æder det i Dag; thi det er Sabbat i Dag for Herren; i Dag skulle I ikke finde det paa Marken.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Seks Dage skulle I sanke det; men paa den syvende Dag, paa Sabbaten, paa den skal det ikke være at finde.
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 Og det skete, paa den syvende Dag gik nogle af Folket ud at sanke, men de fandt intet.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 Da sagde Herren til Mose: Hvor længe vægre I eder ved at holde mine Bud og mine Love?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 Ser, at Herren har givet eder Sabbaten, derfor giver han eder paa den sjette Dag to Dages Brød; bliver hver paa sit Sted, ingen gaa ud fra sit Sted paa den syvende Dag.
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 Og Folket hvilede paa den syvende Dag.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 Og Israels Hus kaldte dets Navn Man; og det var ligesom Korianderfrø hvidt og smagte som Honningkage.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 Og Mose sagde: Dette er det Ord, som Herren befalede: Fyld en Orner deraf til at forvares til eders Efterkommere, paa det de maa se det Brød, som jeg bespiste eder med i Ørken, der jeg udførte eder af Ægyptens Land.
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 Og Mose sagde til Aron: Tag en Krukke, og læg en Orner fuld af Man derudi, og sæt det ned for Herren til at forvares til eders Efterkommere.
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 Ligesom Herren befalede Mose, saa satte Aron det ned for Vidnesbyrdet til at forvares.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 Og Israels Børn aade det Man fyrretyve Aar, til de kom til det Land, som var beboet; de aade Man, indtil de kom til Grænsen af Kanaans Land.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 Men en Orner er den tiende Part af en Efa.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)