< 2 Mosebog 10 >

1 Og Herren sagde til Mose: Gak ind til Farao; thi jeg har forhærdet hans Hjerte og hans Tjeneres Hjerte for at gøre disse mine Tegn iblandt dem,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 og for at du skal forkynde det for dine Børns og dine Børnebørns Øren, hvad jeg har udrettet i Ægypten, og mine Tegn, som jeg har sat iblandt dem; og I skulle fornemme, at jeg er Herren.
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Saa gik Mose og Aron ind til Farao og sagde til ham: Saa siger Herren, Hebræernes Gud: Hvor længe vægrer du dig ved at ydmyge dig for mit Ansigt? lad mit Folk fare, at de maa tjene mig.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 Thi dersom du vægrer dig ved at lade mit Folk fare, se, da vil jeg i Morgen lade Græshopper komme i dit Landemærke.
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 Og de skulle skjule Synet af Jorden, at man ikke skal kunne se Jorden, og de skulle opæde det øvrige, som er reddet, og hvad der er blevet eder tilovers fra Hagelen, og de skulle æde hvert Træ, som vokser op hos eder af Marken.
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 Og dine Huse skulle fyldes og alle dine Tjeneres Huse og alle Ægypternes Huse, hvilket hverken dine Fædre eller dine Forfædre have set, fra den Tid de bleve til paa Jorden indtil denne Dag; saa vendte han sig og gik ud fra Farao.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Da sagde Faraos Tjenere til ham: Hvor længe skal denne være os til en Snare? lad de Mænd fare, at de maa tjene Herren deres Gud; mon du endnu ikke ved, at Ægypten er ødelagt?
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 Og Mose og Aron bleve hentede tilbage til Farao, og han sagde til dem: Gaar, tjener Herren, eders Gud; hvilke ere de, som gaa bort?
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Og Mose sagde: Vi ville gaa med vore unge og vore gamle, med vore Sønner og vore Døtre, med vore Faar og med vore Øksne ville vi gaa; thi det er os Herrens Højtid.
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 Da sagde han til dem: Saa vist være Herren med eder, som jeg vil lade eder og eders smaa Børn fare, ser der, at I have ondt i Sinde.
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 Ikke saa! I Mænd, farer nu hen og tjener Herren, thi det have I begæret; og man drev dem ud fra Faraos Ansigt.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 Da sagde Herren til Mose: Ræk din Haand ud over Ægyptens Land efter Græshopper, og de skulle komme op over Ægyptens Land og æde alle Urter i Landet, ja alt det, som Hagelen lod blive tilovers.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Saa rakte Mose sin Stav over Ægyptens Land, og Herren lod komme Østenvejr i Landet den samme hele Dag og hele Nat; det skete om Morgenen, at Østenvejret bragte Græshopperne op.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 Og der kom Græshopper op over hele Ægyptens Land og lode sig ned i hele Ægyptens Landemærke; de vare i svær Mængde; før dem havde der ikke været Græshopper saaledes, og efter dem skulde der ikke blive saaledes;
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 thi de skjulte Synet af hele Jorden, og Jorden blev formørket, og de aade alle Urter i Landet og al Frugt paa Træerne, som Hagelen lod blive tilovers; og der blev intet grønt tilovers paa Træer eller paa Urter i Marken i hele Ægyptens Land.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Da skyndte Farao sig at kalde ad Mose og Aron, og han sagde: Jeg har syndet imod Herren eders Gud og imod eder.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 Og kære, forlad mig nu min Synd aleneste denne Gang, og beder til Herren eders Gud, at han dog vil borttage denne Død fra mig.
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Og han gik ud fra Farao, og han bad til Herren.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 Og Herren vendte Vejret om til en saare stærk Vestenvind, som førte Græshopperne bort og kastede dem i det røde Hav; der blev ikke een Græshoppe tilovers i hele Ægyptens Landemærke.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 Men Herren forhærdede Faraos Hjerte, og han lod ikke Israels Børn fare.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Og Herren sagde til Mose: Ræk din Haand op mod Himmelen, at der bliver Mørke over Ægyptens Land, at man kan føle paa Mørket.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Og Mose rakte sin Haand op mod Himmelen; da blev der tykt Mørke i hele Ægyptens Land i tre Dage.
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 Ikke een saa den anden, og ingen stod op fra sit Sted i tre Dage; men hos alle Israels Børn var det lyst i deres Boliger.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 Da kaldte Farao ad Mose og sagde: Gaar, tjener Herren, kun skulle I lade eders Faar og Øksne blive; ogsaa eders smaa Børn maa fare med eder.
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Og Mose sagde: Du skal og medgive os Slagtoffere og Brændoffere, at vi kunne ofre til Herren, vor Gud.
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 Og endogsaa vort Fæ skal gaa med os, der skal ikke en Klov blive tilbage; thi vi skulle tage deraf til at tjene Herren, vor Gud; thi vi vide ikke, hvormed vi skulle tjene Herren, førend vi komme derhen.
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 Men Herren forhærdede Faraos Hjerte, og han vilde ikke lade dem fare.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 Og Farao sagde til ham: Gak fra mig, vogt dig, at du ikke mere ser mit Ansigt; thi paa hvilken Dag du ser mit Ansigt, skal du dø.
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Og Mose sagde: Du talede ret; jeg vil herefter ikke mere se dit Ansigt.
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< 2 Mosebog 10 >