< Ester 6 >

1 Iden samme Nat kunde Kongen ikke sove, og han bød at hente Krønikebogen om de daglige Begivenheder; og de bleve læste for Kongen.
A daren nan, sarki bai iya barci ba, saboda haka ya ba da umarni a kawo, a kuma karanta masa littafin tarihi na shekara-shekara, da rubutaccen labarin mulkinsa.
2 Og der fandtes skrevet, at Mardokaj havde gjort Angivelse om Bigtana og Theres, to af Kongens Kammertjenere, af dem, som holdt Vagt ved Dørtærskelen, og som havde søgt at lægge Haand paa Kong Ahasverus.
Aka tarar, a rubuce a ciki, cewa Mordekai ya tone ƙulle-ƙullen Bigtana da Teresh, biyu daga hafsoshin sarki, waɗanda suke tsaron mashigin ƙofa, waɗanda suka ƙulla su kashe Sarki Zerzes.
3 Og Kongen sagde: Hvad Ære og Ophøjelse er der sket Mardokaj for det? Da sagde Kongens Folk, som tjente ham: Ham er ikke sket nogen Ting.
Sarki ya ce, “Wace girma da daraja ce aka ba wa Mordekai saboda wannan?” Masu hidimarsa suka ce, “Ba a yi masa wani abu ba.”
4 Da sagde Kongen: Hvo er i Forgaarden? Og Haman var kommen i Kongens Hus's yderste Forgaard for at tale til Kongen om at hænge Mardokaj paa det Træ, som han havde ladet berede for ham.
Sarki ya ce, “Wa yake a haraba?” Daidai lokacin kuwa Haman ya shigo harabar waje na fada don yă yi magana da sarki a kan a rataye Mordekai a wurin rataye mai laifin da ya shirya.
5 Og Kongens Tjenere sagde til ham: Se, Haman staar i Forgaarden; og Kongen sagde: Lader ham komme ind!
Masu yi wa sarki hidima, suka amsa, “Haman yana tsaye a haraba.” Sarki ya umarta, “A kawo shi ciki.”
6 Der Haman kom, sagde Kongen til ham: Hvad skal man gøre ved den Mand, som Kongen har Lyst til at ære? Og Haman sagde i sit Hjerte: Hvem skulde Kongen have Lyst til at gøre mere Ære end mig?
Sa’an nan Haman ya shigo, sai sarki ya ce masa, “Me ya kamata a yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama?” Haman dai ya yi tunani a ransa ya ce, “Wane ne sarki zai girmama in ba ni ba?”
7 Derfor sagde Haman til Kongen: Er der en Mand, som Kongen har Lyst til at ære,
Sai ya amsa wa sarki cewa, “Saboda mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama,
8 saa bringe man et kongeligt Klædebon, som Kongen har været iført, og en Hest, som Kongen har redet paa, og paa hvis Hoved en kongelig Krone er sat;
bari a kawo rigar sarautar da sarki ya taɓa sawa, da kuma dokin da sarki ya taɓa hawa, wanda aka sa kambin sarauta a kai.
9 og man give det Klædebon og den Hest i Haanden paa en Mand af Kongens fornemste Fyrster, og man iføre den Mand, som Kongen har Lyst til at ære, det, og de skulle lade ham ride paa Hesten igennem Stadens Gader, og de skulle udraabe for hans Ansigt: Saaledes skal man gøre ved den Mand, som Kongen har Lyst til at ære.
Sa’an nan, bari a ba da rigar da kuma dokin wa ɗaya daga cikin manyan sarakuna mafi kirki na sarki. Bari shi kuma yă sa wannan riga wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama, a kuma bi da shi a bisan doki ko’ina a titunan birni, ana shela a gabansa ana cewa, ‘Wannan shi ne abin da ake yin wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!’”
10 Da sagde Kongen til Haman: Skynd dig, tag Klædebonnet og Hesten, som du har talt, og gør saa med Jøden Mardokaj, som sidder ved Kongens Port; undlad ikke noget af alt det, som du har talt!
Sarki ya umarci Haman ya ce, “Tafi yanzu ka karɓi rigar da dokin, ka kuma yi yadda ka shawarta wa Mordekai, mutumin Yahudan nan, wanda yake zama a bakin ƙofar sarki. Kada ka kāsa yin kome daga cikin abin da ka faɗa.”
11 Da tog Haman Klædebonnet og Hesten, lod Mardokaj iføre sig det og lod ham ride igennem Stadens Gader og udraabte for hans Ansigt: Saaledes skal man gøre ved den Mand, som Kongen har Lyst til at ære!
Saboda haka, Haman ya karɓo rigar da dokin. Ya sa wa Mordekai rigar, ya kuma bi da shi a kan doki ko’ina a titunan birnin, yana shela a gabansa yana cewa, “Wannan shi ne abin da ake yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!”
12 Og Mardokaj kom tilbage til Kongens Port; men Haman skyndte sig tilbage til sit Hus, sørgende og med tilhyllet Hoved.
Daga baya, Mordekai ya dawo zuwa ƙofar sarki. Amma Haman ya ruga gida, kansa a rufe, saboda baƙin ciki.
13 Og Haman fortalte Seres, sin Hustru og alle sine Venner alt det, som ham var vederfaret; da sagde hans Vismænd og Seres, hans Hustru, til ham: Dersom Mardokaj, for hvis Ansigt du har begyndt at falde, er af jødisk Æt, da formaar du intet imod ham, men maa aldeles falde for hans Ansigt.
Ya je ya faɗa wa matarsa Zeresh, da dukan abokansa, me ya same shi. Masu ba shi shawara, da matarsa Zeresh, suka ce masa, “Idan Mordekai, wanda ka fara fāɗuwa a gabansa, daga zuriyar Yahudawa yake, to, ba za ka yi nasara a kansa ba, tabbatacce za ka fāɗi a gabansa!”
14 Der de endnu talte med ham, da kom Kongens Kammertjenere til, og de hastede med at føre Haman til Gæstebudet, som Esther havde beredet.
Suna cikin magana da shi ke nan, sai ga bābānnin sarki, suka iso suka kuma hanzarta da Haman zuwa liyafar da Esta ta shirya.

< Ester 6 >