< Prædikeren 12 >

1 Og tænk paa din Skaber i din Ungdoms Dage, førend de onde Dage komme, og de Aar nærme sig, om hvilke du skal sige: Jeg har ikke Lyst til dem:
Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
2 Førend Solen og Lyset og Maanen og Stjernerne formørkes, og Skyerne komme igen efter Regnen;
kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
3 den Dag, da Husets Vogtere bæve, og de stærke Mænd krumme sig, og de, som betjene Møllen, holde op, fordi de ere blevne faa, og de, som se igennem Vinduerne, blive dunkle;
sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
4 da begge Døre til Gaden lukkes, naar Møllens Røst bliver svag, og man staar op ved Fuglens Røst, og alle Sangens Døtre nedbøjes;
sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
5 da de ogsaa frygte for den høje, og der er Rædsler paa Vejen, og Mandeltræet blomstrer, og Græshoppen bliver sig selv til en Byrde, og Begærligheden forgaar; thi Mennesket farer til sit evige Hus, og de sørgende gaa omkring paa Gaden;
sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
6 førend Sølvsnoren borttages, og Guldlampen bliver knust; og Krukken sønderbrydes ved Kilden, og Hjulet sønderslaas ved Brønden;
Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
7 og Støvet kommer til Jorden igen, som det var før, og Aanden kommer til Gud igen, som gav den.
turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
8 Forfængeligheders Forfængelighed! sagde Prædikeren, alt er Forfængelighed!
“Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
9 Og forøvrigt, efterdi Prædikeren var en viis Mand, saa lærte han fremdeles Folket Kundskab og hørte og ransagede og forfattede mange Ordsprog.
Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
10 Prædikeren søgte at finde behagelige Ord, og det, som er skrevet, er Ret, Sandheds Ord.
Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
11 De vises Ord ere som Braadde og som Søm, der trænge dybt ind, I Samlingens Mestre! de ere givne af den ene Hyrde.
Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
12 Og forøvrigt, min Søn! lad dig paaminde af dem; at gøre mange Bøger, saa at der er ingen Ende paa, og megen Læsning trætter Legemet.
Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
13 Enden paa Sagen, naar alting er hørt, er denne: Frygt Gud og hold hans Bud; thi det bør hvert Menneske at gøre.
Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
14 Thi Gud skal føre hver Gerning for Dom med alt det, som er skjult, enten det er godt eller ondt.
Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.

< Prædikeren 12 >