< 5 Mosebog 8 >
1 Iskulle holde alle de Bud, som jeg byder dig i Dag, saa at I gøre derefter, at I maa leve og formeres og komme ind og eje det Land, som Herren har tilsvoret eders Fædre.
Ku hankali, ku bi kowane umarnin da nake ba ku a yau, saboda ku rayu, ku ƙaru, ku kuma shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku.
2 Og du skal ihukomme al den Vej, som Herren din Gud har ladet dig gaa disse fyrretyve Aar i Ørken for at ydmyge dig, for at forsøge dig, for at fornemme, hvad der var i dit Hjerte, om du vilde holde hans Bud eller ej.
Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku a dukan hanya, a cikin hamada waɗannan shekaru arba’in, don yă ƙasƙantar da ku, yă kuma gwada ku don yă san abin da yake a zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa, ko babu.
3 Og han ydmygede dig og lod dig hungre og gav dig Man at æde, hvilket du ikke kendte, og dine Fædre ej kendte, for at lade dig vide, at Mennesket lever ikke ved Brødet alene, men Mennesket lever ved alt det, som udgaar af Herrens Mund.
Ya ƙasƙantar da ku, ya bar ku da yunwa, sa’an nan ya ciyar da ku da Manna, wadda ku, ko kakanninku, ba su sani ba, ta haka ne ya sa kuka sani cewa, ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba, amma ta wurin kowace kalmar da ta fito daga bakin Ubangiji.
4 Dit Klædebon blev ikke gammelt paa dig, og din Fod blev ikke hoven disse fyrretyve Aar.
Tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba a waɗannan shekaru arba’in.
5 Saa kan du kende i dit Hjerte, at ligesom en Mand tugter sin Søn, har Herren din Gud tugtet dig.
Sai ku sani fa a cikin zuciyarku cewa kamar yadda mutum kan horar da ɗansa, haka Ubangiji Allahnku ke horar da ku.
6 Saa hold Herren din Guds Bud, at du vandrer i hans Veje og frygter ham.
Ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuna tafiya cikin hanyoyinsa, kuna kuma girmama shi.
7 Thi Herren din Gud fører dig ind i et godt Land, et Land med Vandbække, Kilder og dybe Brønde, som udvælde i Dalene og paa Bjergene;
Gama Ubangiji Allahnku yana fitar da ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka da tafkunan ruwa, tare da maɓulɓulai masu gudu a kwari da tuddai;
8 et Land med Hvede og Byg og Vintræer og Figentræer og Granatæbletræer, et Land med Olietræer og Honning,
ƙasa mai alkama da sha’ir, inabi da ɓaure, rumman, man zaitun da zuma;
9 et Land, hvor du ikke skal æde Brød i Armod, hvor du ikke skal fattes noget; et Land, hvis Stene ere Jern, og af hvis Bjerge du kan udhugge Kobber.
ƙasa inda abinci ba zai yi ƙaranci ba, ba kuma za ku rasa kome ba; ƙasa ce inda ƙarfe ne duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta.
10 Og du skal æde og blive mæt og love Herren din Gud for det gode Land, som han har givet dig.
Sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda ƙasa mai kyau da ya ba ku.
11 Vogt dig, at du ikke forglemmer Herren din Gud, saa at du ikke holder hans Bud og hans Befalinger og hans Skikke, som jeg byder dig i Dag;
Ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji Allahnku, har ku kāsa kiyaye umarnansa, dokokinsa da ƙa’idodinsa da nake ba ku a wannan rana ba.
12 at du ikke skal æde og blive mæt og bygge gode Huse og bo deri,
To, sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sa’ad da kuka gina gidaje masu kyau, kuka zauna,
13 og dit store Kvæg og dit smaa Kvæg skal formeres, og Sølv og Guld skal formeres for dig, og alt det, som du har, formeres,
sa’ad da kuma garkunanku na shanu da na tumaki suka ƙaru, azurfanku da zinariyarku kuma suka ƙaru, sa’an nan dukan abin da kuke da shi ya haɓaka,
14 og dit Hjerte skulde ophøje sig, og du skulde glemme Herren din Gud, som udførte dig af Ægyptens Land, af Trælles Hus;
to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
15 ham, som ledte dig igennem den store og forfærdelige Ørk, hvor der var giftige Slanger og Skorpioner og Tørhed, hvor der ikke var Vand; ham, som lod Vand udflyde til dig af en haard Stenklippe;
Ya bishe ku cikin hamada mai fāɗi, mai bantsoro, wannan busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa, ga macizai masu dafi da kuma kunamai. Ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara.
16 ham, som gav dig Man at æde i Ørken, hvilket dine Fædre ikke kendte, for at ydmyge dig og for at forsøge dig og at gøre vel imod dig i den sidste Tid;
Ya ba ku Manna don ku ci a cikin hamada, wani abin da kakanninku ba su taɓa sani ba, don yă ƙasƙantar yă kuma gwada ku, saboda yă yi muku alheri daga baya.
17 og du skulde sige i dit Hjerte: Min Kraft og min Haands Styrke har skaffet mig denne Vælde.
Wataƙila ku ce wa kanku, “Ikona da ƙarfin hannuwana ne suka ba ni da wannan arziki.”
18 Men du skal komme Herren din Gud i Hu, thi han er den, som giver dig Kraft til at skaffe dig Vælde, for at stadfæste sin Pagt, som han svor dine Fædre, som det ses paa denne Dag.
Amma ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne wanda yake ba ku azanci na yin arziki, ta haka kuwa ya tabbatar da alkawarinsa, wanda ya rantse wa kakanninku, kamar yadda yake a yau.
19 Og det skal ske, om du glemmer Herren din Gud og vandrer efter andre Guder og tjener og tilbeder dem, da vidner jeg over eder i Dag, at I skulle omkomme.
In kuka manta da Ubangiji Allahnku, kuka kuma bi waɗansu alloli, kuka yi musu sujada, kuka kuma rusuna musu, to, a yau ina gargaɗe ku cewa tabbatacce za a hallaka ku.
20 Ligesom Hedningerne, hvilke Herren lader omkomme for eders Ansigt, saaledes skulle I omkomme, fordi I ikke vilde høre Herren eders Guds Røst.
Kamar al’ummai da Ubangiji ya hallakar kafin ku, haka zai hallaka ku, domin ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku ba.