< 5 Mosebog 6 >

1 Og dette er det Bud, de Skikke og de Befalinger, som Herren eders Gud har budet at lære eder, for at I skulle gøre derefter i Landet, som I drage over til for at eje det;
Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
2 paa det du skal frygte Herren din Gud ved at holde alle hans Skikke og hans Bud, som jeg byder dig, du og din Søn og din Sønnesøn, alle dine Livsdage, og paa det at dine Dage maa forlænges.
saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
3 Og, Israel! du skal høre og bevare dette og gøre derefter, at det maa gaa dig vel, og I maa blive saare mangfoldige, som Herren dine Fædres Gud har sagt dig, i et Land, som flyder med Mælk og Honning.
Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
4 Hør, Israel! Herren vor Gud, Herren er een.
Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
5 Og du skal elske Herren din Gud af dit ganske Hjerte og af din ganske Sjæl og af al din Formue.
Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
6 Og disse Ord, som jeg byder dig i Dag, skulle være paa dit Hjerte.
Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
7 Og du skal indskærpe dine Børn dem og tale om dem, naar du sidder i dit Hus, og naar du gaar paa Vejen, og naar du lægger dig, og naar du staar op.
Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
8 Og du skal binde dem til et Tegn paa din Haand, og de skulle være dig til Spand imellem dine Øjne.
Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
9 Og du skal skrive dem paa Dørstolperne af dit Hus og paa dine Porte.
Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
10 Og det skal ske, naar Herren din Gud fører dig ind i det Land, som han har tilsvoret dine Fædre, Abraham, Isak og Jakob, at ville give dig, store og gode Stæder, som du ikke har bygget,
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
11 og Huse, fulde af alt godt, hvilke du ikke har fyldt, og udhugne Brønde, som du ikke har udhugget, Vingaarde og Oliegaarde, som du ikke har plantet, og du æder og bliver mæt:
gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
12 Saa tag dig i Vare, at du ikke forglemmer Herren, som udførte dig af Ægyptens Land, af Trælles Hus.
ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
13 Du skal frygte Herren din Gud og tjene ham, og ved hans Navn skal du sværge.
Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
14 I skulle ikke gaa efter andre Guder, af de Folks Guder, som ere trindt omkring eder;
Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
15 thi Herren din Gud er en nidkær Gud midt iblandt dig; at Herren din Guds Vrede ikke skal optændes imod dig, og han skal udslette dig fra Jordens Kreds.
gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
16 I skulle ikke friste Herren eders Gud, saaledes som I fristede ham i Massa.
Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
17 I skulle flitteligen holde Herren eders Guds Bud og hans Vidnesbyrd og hans Skikke, som han har budet dig.
Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
18 Og du skal gøre det, som er ret og godt for Herrens Øjne, for at det skal gaa dig vel, og du skal komme ind og eje det gode Land, hvilket Herren har tilsvoret dine Fædre,
Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
19 at han skal udstøde alle dine Fjender for dit Ansigt, som Herren har sagt.
Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
20 Naar din Søn spørger dig herefter og siger: Hvad er det for Vidnesbyrd og Skikke og Befalinger, som Herren vor Gud har budet eder?
Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
21 da skal du sige til din Søn: Vi vare Faraos Trælle i Ægypten, og Herren udførte os af Ægypten med en stærk Haand,
Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
22 og Herren gjorde Tegn og store og fordærvelige Vidundere i Ægypten paa Farao og paa alt hans Hus for vore Øjne,
A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
23 og han udførte os derfra, paa det han vilde føre os ind for at give os det Land, som han havde tilsvoret vore Fædre.
Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
24 Og Herren havde budet os at gøre alle disse Skikke, at frygte Herren vor Gud, at det maa gaa os vel alle Dage, og at han maa holde os ved Live, som det ses paa denne Dag.
Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
25 Og det skal være vor Retfærdighed, naar vi tage Vare paa at gøre efter alle disse Bud for Herren vor Guds Ansigt, som han har budet os.
In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”

< 5 Mosebog 6 >