< 5 Mosebog 33 >

1 Og denne er den Velsignelse, med hvilken Mose den Guds Mand velsignede Israels Børn, førend han døde.
Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
2 Og han sagde: Herren er kommen fra Sinai og er opgangen fra Sejr for dem, han aabenbarede sig herlig fra Parans Bjerg og kom fra de hellige Titusinder; ved hans højre Haand var en brændende Lov til dem.
Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
3 Visseligen, han elsker Folkene; alle hans hellige ere i din Haand; og de skulle sætte sig ved din Fod, annamme af dine Ord.
Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
4 En Lov bød Mose os, en Ejendom for Jakobs Forsamling.
dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
5 Og han blev en Konge for Jeskurun, da Folkets Øverster forsamlede sig tillige med Israels Stammer.
Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
6 Ruben leve og dø ikke; og hans Mænd vorde en liden Hob!
“Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
7 Og dette om Juda: Og han sagde: Hør, Herre! Judas Røst, og lad ham komme til sit Folk; med sine Hænder strider han for det, og vær du en Hjælp mod hans Fjender!
Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
8 Og han sagde om Levi: Dine Thummim og dine Urim høre din fromme Mand til, hvem du fristede i Massa, med hvem du kivedes ved Meribas Vand,
Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
9 ham, som sagde til sin Fader og til sin Moder: Jeg saa ham ikke, og han kendte ikke sine Brødre og vidste ikke af sine Sønner. Thi de holdt dit Ord og bevarede din Pagt;
Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
10 de skulle lære Jakob dine Bud og Israel din Lov; de skulle sætte Røgelse for dit Ansigt og Heloffer paa dit Alter.
Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
11 Herre! velsign hans Kraft og lad hans Hænders Gerning behage dig; knus deres Lænder, som rejse sig imod ham, og deres, som hade ham, saa at de ikke kunne staa op.
Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
12 Han sagde om Benjamin: Herrens elskelige, han skal bo tryggelig hos ham; han skal beskærme ham den ganske Dag, og imellem hans Skuldre skal han bo.
Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
13 Og han sagde om Josef: Hans Land være velsignet af Herren, med Himmelens kostelige Gave, med Duggen, og af Dybet, som ligger her nedenunder,
Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
14 med den kostelige Gave, der bringes frem ved Solen, og med den kostelige Gave, der drives frem ved Maanens Skifter,
da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
15 fra de ældgamle Bjerges Top, og med de evige Højes kostelige Gave,
da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
16 med Jordens og dens Fyldes kostelige Gave, og med Naade fra ham, som boede i Tornebusken; den skal komme over Josefs Hoved og over hans Isse, han er en Fyrste iblandt sine Brødre.
Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
17 Den førstefødte af hans Øksne har Højhed og Horn som Enhjørningens Horn; med dem skal han stange Folkene til Hobe indtil Jordens Ende; og dette er de ti Tusinde af Efraim, og dette er de Tusinde at Manasse.
Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
18 Og han sagde om Sebulon: Glæd dig, Sebulon, i din Udfart, og du Isaskar, i dine Pauluner!
Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
19 De skulle kalde Folkene til Bjerget, der skulle de ofre Retfærdigheds Ofre; thi de skulle suge til sig Havets Overflødighed og Sandets skjulte Skatte.
Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
20 Og han sagde om Gad: Velsignet være den, som udbreder Gad! som en Løve hviler han, og han røver Arm, ja Isse med.
Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
21 Og han udsaa sig den første Lod, thi der var en Førers Lod opbevaret; og han kom til Folkets Øverster, han udøvede Herrens Retfærdighed og hans Befalinger imod Israel.
Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
22 Og han sagde om Dan: Dan er en Løveunge, han springer frem fra Basan.
Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
23 Og om Nafthali sagde han: Nafthali være mæt af Naade og fuld af Herrens Velsignelse; Vesten og Sønden tage han til Eje!
Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
24 Og han sagde om Aser: Aser være velsignet fremfor Sønnerne, han være benaadet blandt sine Brødre og dyppe sin Fod i Olie!
Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
25 Af Jern og Kobber være dine Portslaaer, og som dine Dage din Hvile.
Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
26 Der er ingen som Gud, o Jeskurun! han, som farer paa Himmelen til din Hjælp og med sin Højhed paa de øverste Skyer.
“Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
27 Den evige Gud er en Bolig, og hernede ere de evige Arme; og han har uddrevet Fjenden for dit Ansigt og sagt: Ødelæg!
Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
28 Og Israel bor tryggelig for sig selv; Jakobs Øje er til et Land med Korn og Vin; ja hans Himle skulle dryppe med Dug.
Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
29 Salig er du, Israel! hvo er som du, et Folk, frelst i Herren, han er din Hjælps Skjold og din Højheds Sværd! og dine Fjender skulle smigre for dig, og du skal træde paa deres Høje.
Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”

< 5 Mosebog 33 >