< 5 Mosebog 26 >

1 Og det skal ske, naar du kommer ind i det Land, som Herren din Gud giver dig til Arv, og du ejer det og bor derudi:
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
2 Da skal du tage af det første af al Jordens Frugt, som du bringer ind af dit Land, hvilket Herren din Gud giver dig, og lægge det i en Kurv; og du skal gaa til det Sted, som Herren din Gud skal udvælge til der at lade sit Navn bo.
sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
3 Og du skal komme til Præsten, som er i de Dage, og sige til ham: Jeg forkynder i Dag for Herren din Gud, at jeg er kommen i det Land, som Herren tilsvor vore Fædre at give os.
ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
4 Og Præsten skal tage Kurven af din Haand, og han skal sætte den ned foran Herren din Guds Alter.
Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
5 Da skal du vidne og sige for Herren din Guds Ansigt: Min Fader var en omvankende Syrer, og han drog med nogle faa Mennesker ned til Ægypten og var fremmed der, og han blev der til et stort, stærkt og mangfoldigt Folk.
Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
6 Men Ægypterne handlede ilde med os og plagede os og lagde en haard Trældom paa os.
Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
7 Da skrege vi til Herren, vore Fædres Gud, og Herren hørte vor Røst og saa vor Trængsel og vor Møje og vor Nød;
Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
8 og Herren udførte os af Ægypten med en stærk Haand og udrakt Arm og med en stor Rædsel og med Tegn og med underlige Gerninger.
Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
9 Og han førte os til dette Sted, og han har givet os dette Land, et Land, som flyder med Mælk og Honning.
Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
10 Og nu, se, jeg har ført hid det første af Frugten i Landet, som du, Herre, har givet mig. Og du skal lade det blive for Herren din Guds Ansigt og tilbede for Herren din Guds Ansigt.
yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
11 Og du skal være glad over alt det gode, som Herren din Gud har givet dig og dit Hus, du og Leviten og den fremmede, som er midt iblandt dig.
Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
12 Naar du er færdig med at tiende al Tienden af din Afgrøde i det tredje Aar, som er Tiendens Aar, og du har givet Leviten, den fremmede, den faderløse og Enken, at de maa æde inden dine Porte og blive mætte:
Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
13 Da skal du sige for Herren din Guds Ansigt: Jeg har borttaget det helligede af Huset, og jeg har ogsaa givet Leviten og den fremmede, den faderløse og Enken det, efter alle dine Bud, som du har budet mig; jeg har ikke overtraadt og ikke glemt noget af dine Bud.
Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
14 Jeg har intet ædet deraf i min Sorg og intet borttaget deraf under Urenhed, jeg har intet deraf givet for en afdød; jeg har været Herren min Guds Røst lydig, jeg har gjort alt det, som du har budet mig.
Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
15 Se ned fra din Helligheds Bolig fra Himmelen, og velsign dit Folk Israel og det Land, som du har givet os, ligesom du har tilsvoret vore Fædre, et Land, som flyder med Mælk og Honning.
Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
16 Herren din Gud byder dig paa denne Dag at gøre efter disse Skikke og Bud, og du skal holde dem og gøre efter dem af dit ganske Hjerte og af din ganske Sjæl.
Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
17 Du har i Dag tilsagt Herren, at han skal være din Gud, og at du vil vandre i hans Veje og holde hans Skikke og hans Bud og hans Love, og at du vil høre hans Røst.
Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
18 Og Herren har tilsagt dig i Dag, at du skal være ham et Ejendomsfolk, saasom han har talet til dig, og at du skal holde alle hans Bud,
Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
19 og at han vil sætte dig højt over alle Folk, hvilke han har skabt, til Lov og til Navnkundighed og til Pryd, og at du skal være Herren din Gud et helligt Folk, saasom han har talet.
Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.

< 5 Mosebog 26 >