< 5 Mosebog 17 >

1 Du skal ikke ofre Herren din Gud Okse eller Lam, som har en Lyde, eller nogen slem Ting; thi det er Herren din Gud en Vederstyggelighed.
Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
2 Naar der findes midt iblandt dig, i en af dine Byer, som Herren din Gud giver dig, Mand eller Kvinde, som gør det, som er ondt for Herren din Guds Øjne, ved at overtræde hans Pagt,
In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
3 og denne gaar hen og tjener andre Guder og tilbeder dem, enten Sol eller Maane eller noget af hele Himmelens Hær, som jeg ikke har budet,
wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
4 og det bliver givet dig til Kende, og du hører det: Da skal du ransage det vel; og se, er det Sandhed, er det Ord vist, er denne Vederstyggelighed sket i Israel:
in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
5 Da skal du føre den Mand eller den Kvinde, som gjorde denne onde Handel, ud til dine Porte, Manden eller Kvinden, og du skal stene dem med Sten, og de skulle dø.
sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
6 Efter to Vidners eller tre Vidners Mund skal den lide Døden, som er skyldig at dø; han skal ikke lide Døden efter eet Vidnes Mund.
Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
7 Vidnernes Haand skal først være paa ham til at slaa ham ihjel og til sidst alt Folkets Haand; saa skal du borttage den onde af din Midte.
Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
8 Naar en Sag for Retten er for vanskelig for dig, imellem Blod og Blod, imellem Sag og Sag og imellem Slag og Slag, i hvad Retstrætte der kan være inden dine Porte: Da skal du gøre dig rede og gaa op til det Sted, som Herren din Gud skal udvælge.
In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
9 Og du skal komme til Præsterne, Leviterne og til den Dommer, som mon være i de samme Dage; og du skal forespørge dig, saa skulle de give dig Rettens Ord til Kende.
Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
10 Og du skal gøre efter det Ords Lydelse, som de give dig til Kende fra det Sted, som Herren skal udvælge, og du skal tage Vare paa, at du gør efter alt det, som de lære dig.
Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
11 Efter den Lovs Lydelse, som de lære dig, og efter den Ret, som de sige dig, skal du gøre; du skal ikke vige fra det Ord, som de tilkendegive dig, hverken til højre eller til venstre Side.
Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
12 Men den Mand, som gør noget i Hovmodighed, at han ikke vil høre Præsten, som staar til at tjene der for Herren din Gud, eller Dommeren, den Mand skal dø, og du skal borttage den onde af Israel,
Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
13 for at alt Folket maa høre det og frygte og ikke mere handle hovmodigen.
Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
14 Naar du kommer i det Land, som Herren din Gud giver dig, og ejer det og bor deri, og du siger: Jeg vil sætte en Konge over mig ligesom alle Folkene, som ere trindt omkring mig,
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
15 da skal du sætte den til Konge over dig, som Herren din Gud skal udvælge; du skal sætte en af dine Brødres Midte til Konge over dig, du maa ikke sætte over dig en fremmed Mand, som ikke er din Broder.
ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
16 Kun skal han ikke holde mange Heste og ikke komme Folket til at drage tilbage til Ægypten for at hente mange Heste; thi Herren har sagt eder: I skulle ikke herefter ydermere drage tilbage ad denne Vej.
Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
17 Han skal ikke heller tage sig mange Hustruer, at hans Hjerte ikke skal afvige; han skal ikke heller samle sig saare meget Sølv og Guld.
Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
18 Og det skal ske, naar han sidder paa sit Riges Trone, da skal han lade sig skrive en Afskrift af denne Lov i en Bog efter den, som er hos Præsterne, Leviterne.
Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
19 Og den skal være hos ham, og han skal læse i den alle sit Livs Dage, paa det han kan lære at frygte Herren sin Gud, at holde alle denne Lovs Ord og disse Skikke og gøre efter dem,
Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
20 for at hans Hjerte ikke skal ophøje sig over hans Brødre, ej heller vige fra Budet til højre eller venstre Side, for at han maa forlænge sine Dage i sit Kongerige, han og hans Børn i Israel.
don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.

< 5 Mosebog 17 >