< Daniel 12 >
1 Og paa den Tid skal Mikael, den store Fyrste, der staar som Værn for dit Folks Børn, staa frem, og der skal være en Trængsels Tid, som aldrig har været, siden Folk blev til og indtil den Tid; og paa samme Tid skal dit Folk undkomme, hver den, som findes skreven i Bogen.
“A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
2 Og mange af dem, som sove i Støvets Jord, skulle opvaagne, somme til et evigt Liv, og somme til Skam, til evig Afsky.
Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
3 Men de forstandige skulle skinne som den udstrakte Befæstnings Skin; og de, der førte de mange til Retfærdighed, som Stjernerne evindelig og altid.
Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
4 Og du, Daniel, luk til for Ordene, og forsegl Bogen indtil Endens Tid; mange skulle søge ivrigt i den, og Kundskab skal blive mangfoldig.
Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
5 Og jeg, Daniel, jeg saa, og se, der stod to andre, een her paa Bredden af Floden, og een der paa Bredden af Floden.
Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
6 Og der blev sagt til den Mand, som var iført de linnede Klæder, og som stod oven over Flodens Vande: Hvor længe skal det vare med Enden paa disse underfulde Ting?
Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
7 Og jeg hørte Manden, som var iført de linnede Klæder, og som stod oven over Flodens Vande, og han opløftede sin højre Haand og sin venstre Haand imod Himlene og svor ved ham, som lever evindelig: Igennem een Tid, Tider og en halv Tid, og naar det hellige Folks Magt fuldstændigt er knust, skulle alle disse Ting fuldendes.
Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
8 Og jeg hørte det, men forstod det ikke; og jeg sagde: Min Herre! hvad er det sidste af dette?
Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
9 Og han sagde: Gak bort, Daniel! thi Ordene skulle være tillukkede og forseglede indtil Endens Tid.
Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
10 Mange skulle rense sig og to sig hvide og lutre sig, men de ugudelige skulle handle ugudeligt, og ingen af de ugudelige skal forstaa det; men de forstandige skulle forstaa det.
Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
11 Og fra den Tid, da den stadige Tjeneste bliver borttagen, og det for at opstille Ødelæggelsens Vederstyggelighed, er der Tusinde to Hundrede og halvfemsindstyve Dage.
“Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
12 Salig er den, som bier og naar til Tusinde tre Hundrede fem og tredive Dage.
Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
13 Men gak du dit Endeligt i Møde, og hvil, og staa frem til din Lod ved Dagenes Ende!
“Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”