< Amos 9 >

1 Jeg saa Herren staa over Alteret, og han sagde: Slaa Søjlehovederne, saa at Dørtærsklerne ryste, og slaa dem itu ned over alles Hoved, og de overblevne af dem skal jeg ihjelslaa med Sværdet; af dem skal ingen, som flyr, undfly, og af dem skal ingen, som undkommer, reddes.
Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
2 Om de end bore sig ned i Dødsriget, skal dog min Haand hente dem, derfra; og om de end fare op til Himmelen, skal jeg dog kaste dem ned derfra. (Sheol h7585)
Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
3 Og om de end skjule sig paa Karmels Top, skal jeg dog oplede dem og hente dem derfra; og om de skjule sig for mine Øjne paa Havets Bund, skal jeg dog derfra befale Slangen, at den skal bide dem.
Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
4 Og om de end gaa som Fanger for deres Fjenders Ansigt, skal jeg dog derfra befale Sværdet, at det skal ihjelslaa dem; og jeg vil gette mit Øje imod dem til det onde, og ikke til det gode.
Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
5 Og den Herre, Herre Zebaoth, han rører ved Jorden, og den smelter, saa at alle, som bo derpaa, sørge, og den helt hæver sig som Floden og sænker sig som Ægyptens Flod.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
6 Han er den, som bygger sin Trone i Himmelen og grundfæster sin Hvælving over Jorden; han er den, som kalder ad Vandene i Havet og udøser dem over Jordens Overflade; Herren er hans Navn.
shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
7 Mon I ikke ere mig som Morianers Børn, o Israels Børn? siger Herren; mon jeg ikke har ført Israel op fra Ægyptens Land og Filisterne fra Kafthor og Syrerne fra Kir?
“Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
8 Se, den Herres, Herres Øjne ere imod det syndige Rige, og jeg vil udslette det af Jordens Overflade; dog vil jeg ikke aldeles udslette Jakobs Hus, siger Herren.
“Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
9 Thi se, jeg byder og ryster Israels Hus om iblandt alle Folkene, ligesom der rystes om i et Sold, og der ikke falder eet Korn til Jorden.
“Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
10 Alle Syndere iblandt mit Folk skulle dø ved Sværdet, de, søm sige: Ulykken skal ikke nærme sig eller komme til os.
Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
11 Paa denne Dag vil jeg oprejse Davids faldne Hytte, og jeg vil opmure Bruddene derpaa og oprejse det nedrevne deraf og bygge den som i fordums Dage,
“A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
12 for at de skulle arve det overblevne af Edom og alle de Folkeslag, over hvilke mit Navn nævnes, siger Herren, som gør dette.
domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
13 Se, de Dage komme, siger Herren, da Plovmanden skal naa Høstmanden, og den, som træder Vindruer, skal naa den, som udsaar Sæden, og Bjergene skulle dryppe med Most og alle Højene flyde.
“Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
14 Og jeg vil omvende mit Folk Israels Fangenskab, og de skulle bygge de ødelagte Stæder og tage Bolig der og plante Vingaarde og drikke Vinen af dem, og de skulle anlægge Haver og æde Frugten af dem.
Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
15 Og jeg vil plante dem i deres Land; og de skulle ikke ydermere oprykkes af deres Land, som jeg har givet dem, siger Herren din Gud.
Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.

< Amos 9 >