< Amos 5 >

1 Hører dette Ord, som jeg opløfter over eder, en Klagesang, o Israels Hus!
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 Hun er falden, ej mere skal hun rejse sig, hun, Israels Jomfru! hun er nedkastet paa sin Jord, der er ingen, som rejser hende.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 Thi saa siger den Herre, Herre: Den Stad, af hvilken tusinde gik ud, skal beholde hundrede tilovers; og den, af hvilken hundrede gik ud, skal beholde ti tilovers, i hele Israels Hus.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 Thi saa siger Herren til Israels Hus: Søger mig, saa skulle I leve.
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 Og søger ikke Bethel, og kommer ikke til Gilgal, og gaar ikke over til Beersaba; thi Gilgal skal bortføres, og Bethel skal blive til intet.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Søger Herren, saa skulle I leve, at han ikke som en Ild skal drage over Josefs Hus, og den skal fortære, og der skal ingen være, som slukker i Bethel.
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 De, som omvende Ret til Malurt og kaste Retfærdighed til Jorden!
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 Han skaber Syvstjernen og Orion og omvender Dødens Skygge til Morgen og formørker Dagen til Nat, han, som kalder ad Havets Vande, og udøser dem over Jordens Overflade — „Herren” er hans Navn —
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 han, som lader Ødelæggelse bryde frem over den stærke og Ødelæggelse komme over Befæstningen!
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 De hade i Porten den, som viser til Rette, og den, som taler oprigtigt, afsky de.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Derfor, fordi I træde paa den fattige og tage en svar Afgift i Korn af ham, saa have I vel bygget Huse af hugne Sten, men I skulle ikke bo i dem; I have plantet lystelige Vingaarde, men I skulle ikke drikke Vin af dem.
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 Thi jeg ved, at eders Overtrædelser ere mange, og at eders Synder ere svare, idet I trænge den retfærdige, tage Sonepenge og bøje Retten for de fattige i Porten.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 Derfor maa den, som er klog, tie i denne Tid; thi det er en ond Tid.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Søger det gode og ikke det onde, paa det I maa leve; og saa skal den Herre Zebaoths Gud være med eder, saaledes som I sige.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Hader det onde, og elsker det gode, og hævder Retten i Porten; maaske Herren, den Zebaoths Gud, maatte vorde det overblevne af Josef naadig.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 Derfor, saa siger Herren, den Herre, Zebaoths Gud: Der skal være Klage paa alle Gader, og de skulle sige i alle Stræder: Ve, ve! og de skulle kalde Agerdyrkeren ind til Sorg og til Klage dem, som forstaa sig paa at jamre.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 Og i alle Vingaarde skal der være Klage; thi jeg vil drage midt over dig, siger Herren.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Ve dem, som begære Herrens Dag! hvortil skal Herrens Dag være eder? den er Mørke og ikke Lys;
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 ligesom naar een flyr for Løven, og der da møder ham en Bjørn, og naar han er kommen i Huset og støtter sig med sin Haand til Væggen, der da en Slange bider ham.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Er ikke Herrens Dag Mørke uden Lys? og bælgmørk uden Skin paa den?
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 Jeg hader, jeg foragter eders Fester, og jeg finder ikke Behag i eders Højtidsforsamlinger.
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 Thi om I end ofre mig Brændofre, saa har jeg dog ikke Behag i eders Gaver; og jeg ser ikke hen til Takoffer af eders fede Kvæg.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Tag bort fra mig dine Sanges Brusen; dine Harpers Toner gider jeg ikke høre.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 Men Retten skal bølge frem som Vandene og Retfærdighed som en stedse rindende Bæk.
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Mon I have bragt mig Slagtofre og Madofre i Ørken i fyrretyve Aar, o Israels Hus!
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 Men I have baaret eders Konges Hytte og eders Billeders Opstilling, eders Guds Stjerne, som I havde gjort eder.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 Og jeg vil bortføre eder ud hinsides Damaskus, siger Herren, Zebaoths Gud er hans Navn.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.

< Amos 5 >