< Apostelenes gerninger 14 >
1 Men det skete i Ikonium, at de sammen gik ind i Jødernes Synagoge og talte saaledes, at en stor Mængde, baade af Jøder og Grækere, troede.
A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
2 Men de Jøder, som vare genstridige, ophidsede Hedningernes Sind og satte ondt i dem imod Brødrene.
Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
3 De opholdt sig nu en Tid lang der og talte med Frimodighed i Herren, som gav sin Naades Ord Vidnesbyrd, idet han lod Tegn og Undere ske ved deres Hænder.
Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
4 Men Mængden i Byen blev uenig, og nogle holdt med Jøderne, andre med Apostlene.
Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
5 Men da der blev et Opløb, baade af Hedningerne og Jøderne med samt deres Raadsherrer, for at mishandle og stene dem,
Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
6 og de fik dette at vide, flygtede de bort til Byerne i Lykaonien, Lystra og Derbe, og til det omliggende Land,
Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
7 og der forkyndte de Evangeliet.
inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
8 Og i Lystra sad der en Mand, som var kraftesløs i Fødderne, lam fra Moders Liv, og han havde aldrig gaaet.
A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
9 Han hørte Paulus tale; og da denne fæstede Øjet paa ham og saa, at han havde Tro til at frelses, sagde han med høj Røst:
Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
10 „Staa ret op paa dine Fødder!” Og han sprang op og gik omkring.
sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
11 Men da Skarerne saa, hvad Paulus havde gjort, opløftede de deres Røst og sagde paa Lykaonisk: „Guderne ere i menneskelig Skikkelse stegne ned til os.”
Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
12 Og de kaldte Barnabas Zeus, men Paulus Hermes, fordi han var den, som førte Ordet.
Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
13 Men Præsten ved Zeustemplet, som var uden for Byen, bragte Tyre og Kranse hen til Portene og vilde ofre tillige med Skarerne.
Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
14 Men da Apostlene, Barnabas og Paulus, hørte dette, sønderreve de deres Klæder og sprang ind i Skaren,
Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
15 raabte og sagde: „I Mænd! hvorfor gøre I dette? Vi ere ogsaa Mennesker, lige Kaar undergivne med eder, og vi forkynde eder Evangeliet om at vende om fra disse tomme Ting til den levende Gud, som har gjort Himmelen og Jorden og Havet og alt, hvad der er i dem;
“Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
16 han, som i de forbigangne Tider lod alle Hedningerne vandre deres egne Veje,
A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
17 ihvorvel han ikke lod sig selv være uden Vidnesbyrd, idet han gjorde godt og gav eder Regn og frugtbare Tider fra Himmelen og mættede eders Hjerter med Føde og Glæde.”
Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
18 Og det var med Nød og næppe, at de ved at sige dette afholdt Skarerne fra at ofre til dem.
Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
19 Men der kom Jøder til fra Antiokia og Ikonium, og de overtalte Skarerne og stenede Paulus og slæbte ham uden for Byen i den Tro, at han var død.
Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
20 Men da Disciplene omringede ham, stod han op og gik ind i Byen. Og den næste Dag gik han med Barnabas bort til Derbe.
Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
21 Og da de havde forkyndt Evangeliet i denne By og vundet mange Disciple, vendte de tilbage til Lystra og Ikonium og Antiokia
Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
22 og styrkede Disciplenes Sjæle og paamindede dem om at blive i Troen og om, at vi maa igennem mange Trængsler indgaa i Guds Rige.
suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
23 Men efter at de i hver Menighed havde udvalgt Ældste for dem, overgave de dem under Bøn og Faste til Herren, hvem de havde givet deres Tro.
Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
24 Og de droge igennem Pisidien og kom til Pamfylien.
Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
25 Og da de havde talt Ordet i Perge, droge de ned til Attalia.
kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
26 Og derfra sejlede de til Antiokia, hvorfra de vare blevne overgivne til Guds Naade til den Gerning, som de havde fuldbragt.
Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
27 Men da de kom derhen og havde forsamlet Menigheden, forkyndte de, hvor store Ting Gud havde gjort med dem, og at han havde aabnet en Troens Dør for Hedningerne.
Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
28 Men de opholdt sig en ikke liden Tid sammen med Disciplene.
Suka kuma jima a can tare da almajirai.