< 2 Samuel 8 >

1 Og det skete derefter, at David slog Filisterne og ydmygede dem, og David tog Metheg-Ha-Amma ud af Filisternes Haand.
Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
2 Og han slog Moabiterne og maalte dem med en Snor, idet han lod dem lægge sig paa Jorden, og han maalte to Snore fulde til at slaa ihjel, og en Snor fuld til at lade leve; saa bleve Moabiterne Davids Tjenere, og de bragte ham Skænk.
Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
3 David slog og Hadad-Eser, Rekobs Søn, Kongen i Zoba, der denne drog hen at vende sin Haand mod Floden Frat.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
4 Og David tog fra ham tusinde og syv Hundrede Ryttere og tyve Tusinde Mand Fodfolk, og David lammede alle Vognheste og lod hundrede Heste blive tilovers af dem.
Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
5 Men Syrerne af Damaskus kom for at hjælpe Hadad-Eser, Kongen af Zoba, og David slog af Syrerne to og tyve Tusinde Mænd.
Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
6 Og David lagde Besætning i det damascenske Syrien; saa bleve Syrerne Davids Tjenere, som bragte ham Skænk; og Herren frelste David, ihvor han drog hen.
Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
7 Og David tog de Guldskjolde, som vare hos Hadad-Esers Tjenere, og førte dem til Jerusalem.
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
8 Men af Betha og af Berothaj, Hadad-Esers Stæder, tog Kong David saare meget Kobber.
Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
9 Der Thoi, Kongen af Hamath, hørte, at David havde slaget hele Hadad-Esers Hær,
Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
10 da sendte Thoi sin Søn Joram til Kong David for at hilse ham og for at velsigne ham, fordi han havde stridt imod Hadad-Eser og slaget ham; thi Hadad-Eser førte stedse Krig imod Thoi; og han havde Sølvkar og Guldkar og Kobberkar med sig.
sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
11 Ogsaa dem helligede Kong David for Herren, tillige med det Sølv og det Guld, som han helligede fra alle de Hedninger, som han havde undertvunget,
Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
12 fra Syrien og fra Moab og fra Ammons Børn og fra Filisterne og fra Amalek og af Byttet fra Hadad-Eser, Rekobs Søn, Kongen af Zoba.
wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
13 Og David gjorde sig navnkundig, der han kom tilbage, efter at han havde slaget Syrerne, og (slog af Edomiterne) udi Saltdalen atten Tusinde.
Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
14 Og han lagde Besætning udi Edom, udi hele Edom lagde han Besætning, og alle Edomiterne bleve Davids Tjenere; og Herren frelste David, ihvor han drog hen.
Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
15 Saa var David Konge over al Israel, og David gjorde Ret og Retfærdighed for alt sit Folk.
Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
16 Og Joab, Zerujas Søn, var over Hæren, og Josafat, Ahiluds Søn, var Historieskriver;
Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
17 og Zadok, Ahitubs Søn, og Akimelek, Abjathars Søn, vare Præster, og Seraja var Skriver;
Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
18 og Benaja, Jojadas Søn, var over de Krethi og de Plethi, og Davids Sønner vare hans ypperste Raad.
Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.

< 2 Samuel 8 >