< 2 Samuel 6 >
1 Derefter samlede David atter alle udvalgte i Israel, tredive Tusinde.
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 Og David gjorde sig rede og gik hen, han og alt Folket, som var hos ham, fra Baale-Juda, for derfra at føre Guds Ark op, over hvilken der nævnes et Navn, den Herre Zebaoths Navn, som sidder over Keruber.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 Og de førte Guds Ark paa en ny Vogn og toge den fra Abinadabs Hus, som var paa Højen; men Ussa og Ahio, Abinadabs Sønner, førte den nye Vogn.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 Saa toge de den fra Abinadabs Hus, som var paa Højen, og fulgte med Guds Ark; men Ahio gik foran Arken.
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 Da legede David og alt Israels Hus for Herrens Ansigt med alle Haande Strengeleg af Fyrretræ, med Harper og med Citere og med Trommer og med Bjælder og med Cymbler.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 Og der de kom til Nakons Lade, da udrakte Ussa Haanden til Guds Ark og greb fat paa den; thi Øksnene vege ud af Sporet.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 Da optændtes Herrens Vrede imod Ussa, og Gud slog ham der for hans Forseelses Skyld, og han døde der ved Guds Ark.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 Da blev David ilde tilfreds, fordi Herren havde gjort et Skaar paa Ussa, og man kaldte det Sted Perez-Ussa indtil denne Dag.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 Og David frygtede for Herren samme Dag og sagde: Hvorledes skal Herrens Ark komme til mig?
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 Og David vilde ikke føre Herrens Ark til sig i Davids Stad; men David lod den føre hen til Githiteren Obed-Edoms Hus.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 Og Herrens Ark blev tre Maaneder i Githiteren Obed-Edoms Hus, og Herren velsignede Obed-Edom og alt hans Hus.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 Og det blev Kong David tilkendegivet, idet der sagdes: Herren har velsignet Obed-Edoms Hus og alt det, han har, for Guds Arks Skyld; da gik David hen og førte Guds Ark op af Obed-Edoms Hus til Davids Stad med Glæde.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 Og det skete, naar de, som bare Herrens Ark, vare gaaede seks Trin, da ofrede man Øksne og fedt Kvæg.
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 Og David dansede af alle Kræfter for Herren Ansigt, og David var iført en linnet Livkjortel.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 Saa førte David og alt Israels Hus Herrens Ark op med Frydeskrig og med Basuns Lyd.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 Og det skete, der Herrens Ark kom i Davids Stad, da saa Mikal, Sauls Datter, ud igennem Vinduet og saa Kong David springe af alle Kræfter for Herrens Ansigt, og hun foragtede ham i sit Hjerte.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 Og de førte Herrens Ark ind og satte den paa sit Sted midt i Paulunet, som David havde opslaaet til den; og David ofrede Brændofre og Takofre for Herrens Ansigt.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 Der David var færdig med at ofre Brændofre og Takofre, da velsignede han Folket i den Herre Zebaoths Navn.
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 Og han uddelte til alt Folket og til al Israels Mangfoldighed, baade Mand og Kvinde, til hver en Brødkage og et godt Stykke Kød og en Rosinkage; da gik alt Folket bort, hver til sit Hus.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 Der David kom tilbage for at velsigne sit Hus, da gik Mikal, Sauls Datter, ud imod David og sagde: Hvor æret var Israels Konge i Dag, som blottede sig i Dag for sine Tjeneres Tjenestepigers Øjne, ligesom en af løse Folk ubluelig blotter sig.
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 Da sagde David til Mikal: Det gjorde jeg for Herrens Ansigt, hans, som mig udvalgte fremfor din Fader og fremfor alt hans Hus, saa han befalede mig at være en Fyrste over Herrens Folk, over Israel, og jeg har leget for Herrens Ansigt.
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 Og jeg vil endnu blive ringere end saa og ydmyge mig i mine egne Øjne; og de Tjenestepiger, som du talede om, med dem vil jeg æres.
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 Men Mikal, Sauls Datter, fik ikke noget Barn indtil sin Dødsdag.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.