< 2 Samuel 5 >
1 Da kom alle Israels Stammer til David i Hebron, og de sagde saaledes: Se, her ere vi, vi ere dine Ben og dit Kød.
Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
2 Ogsaa tilforn, der Saul var Konge over os, da var du den, som førte Israel ud og ind; saa har Herren sagt til dig: Du skal vogte mit Folk Israel, og du skal være Fyrste over Israel.
A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
3 Og alle de Ældste af Israel kom til Kongen i Hebron, og Kong David gjorde en Pagt med dem i Hebron for Herrens Ansigt, og de salvede David til Konge over Israel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
4 David var tredive Aar gammel, der han blev Konge, han regerede fyrretyve Aar.
Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
5 Han regerede i Hebron over Juda syv Aar og seks Maaneder og regerede i Jerusalem i tre og tredive Aar over hele Israel og Juda.
A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
6 Og Kongen drog hen og hans Mænd til Jerusalem imod Jebusiterne, som boede i Landet; og de sagde til David: Du skal ikke komme herind, men de blinde og lamme skulle drive dig bort; hvormed de vilde sige: David skal ikke komme herind.
Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
7 Men David indtog Zions Befæstning, det er Davids Stad.
Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
8 Thi David havde sagt paa den samme Dag: Hvo som helst der slaar Jebusiterne og naar til Vandrenden og slaar de halte og de blinde, som ere Davids Sjæl forhadte —; derfor siger man: En blind eller en lam skal ikke komme ind i Huset.
A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
9 Saa boede David i Befæstningen og kaldte den Davids Stad, og David byggede trindt omkring fra Millo af og indadtil.
Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
10 Og David gik stedse frem og blev stor; thi Herren Zebaoths Gud var med ham.
Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
11 Og Hiram, Kongen af Tyrus, sendte Bud til David med Cedertræ og Mestre til at udhugge i Træ og Mestre til at udhugge i Sten til Vægge, og de byggede David et Hus.
To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
12 Og David fornam, at Herren havde stadfæstet ham til Konge over Israel, og at han havde ophøjet hans Kongedømme for sit Folk Israels Skyld.
Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
13 Og David tog endnu Medhustruer og Hustruer af Jerusalem, efter at han var kommen fra Hebron; og der fødtes endnu Sønner og Døtre for David.
Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
14 Og disse ere deres Navne, som ham fødtes i Jerusalem: Sammua og Sobab og Nathan og Salomo
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
15 og Jibkar og Elisua og Nefeg og Jafla
Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
16 og Elisama og Eljada og Elifelet.
Elishama, Eliyada da Elifelet.
17 Der Filisterne hørte, at de havde salvet David til Konge over Israel, da droge alle Filisterne op for at søge efter David; der David hørte det, da drog han ned til Befæstningen.
Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
18 Og Filisterne kom, og de spredte sig i Refaims Dal.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
19 Og David spurgte Herren ad og sagde: Skal jeg drage op imod Filisterne? vil du give dem i min Haand? Og Herren sagde til David: Drag op, thi jeg vil give Filisterne i din Haand.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
20 Og David kom til Baal-Perazim, og David slog dem der og sagde: Herren har brudt igennem mine Fjender for mit Ansigt, som Vand bryder igennem; derfor kalder man det samme Steds Navn Baal-Perazim.
Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
21 Og de efterlode deres Afguder der, og David og hans Mænd toge dem op.
Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
22 Men Filisterne bleve endnu ved at drage op og spredte sig i Refaims Dal.
Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
23 Og David spurgte Herren ad, men han sagde: Du skal ikke drage op; men kom omkring bag paa dem, at du kommer til dem tværs over for Morbærtræerne.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
24 Og det skal ske, naar du hører en Lyd af en Skriden hen over Morbærtræernes Toppe, da maa du røre dig; thi da er Herren udgangen for dit Ansigt til at slaa Filisternes Lejr.
Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
25 Og David gjorde saaledes, ligesom Herren havde befalet ham, og slog Filisterne fra Geba indtil hen imod Geser.
Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.