< 2 Samuel 24 >
1 Og Herrens Vrede optændtes atter imod Israel, og han tilskyndte David imod dem, at han sagde: Gak hen, tæl Israel og Juda.
Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
2 Og Kongen sagde til Joab, Stridshøvedsmanden, som var hos ham: Kære, gak omkring i alle Israels Stammer, fra Dan og indtil Beersaba, og tæller Folket, at jeg kan vide Folkets Tal.
Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
3 Og Joab sagde til Kongen: Gid Herren din Gud vilde lægge til dette Folk hundrede Gange saa mange, som disse og disse ere, og min Herre Kongens Øjne maatte se det; men hvorfor har min Herre Kongen Lyst til denne Gerning?
Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
4 Men Kongens Ord fik Overhaand imod Joab og imod Høvedsmændene for Hæren; saa drog Joab ud og Høvedsmændene for Hæren fra Kongens Ansigt til at tælle Folket Israel.
Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
5 Og de gik over Jordanen, og de lejrede sig i Aroer paa den højre Side af Staden, som ligger midt i Gads Dal, og Jaeser.
Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
6 Og de kom til Gilead og til det nedenfor liggende Land, som nylig var indtaget, og de kom til Dan-Jaan og trindt omkring til Zidon.
Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
7 Og de kom til den faste Stad Tyrus og til alle Heviternes og Kananiternes Stæder, og de gik ud imod Sønden i Juda indtil Beersaba.
Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
8 Og de gik omkring i alt Landet og kom, der ni Maaneder og tyve Dage vare til Ende, til Jerusalem.
Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
9 Og Joab overgav Tallet paa Folket, som var talt, til Kongen, og der var i Israel otte Hundrede Tusinde stridbare Mænd, som kunde uddrage Sværd, og Judas Mænd vare fem Hundrede Tusinde Mand.
Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
10 Da slog Davids Hjerte ham, efter at han havde talt Folket, og David sagde til Herren: Jeg har saare syndet, at jeg har gjort det, og nu, Herre, kære, borttag din Tjeners Misgerning; thi jeg har handlet meget daarligt.
Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
11 Og der David stod op om Morgenen, da skete Herrens Ord til Gad, Profeten, Davids Seer, og han sagde:
Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
12 Gak og sig til David: Saa sagde Herren: Jeg lægger dig tre Ting for, udvælg dig en af dem, den vil jeg gøre dig.
“Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
13 Og Gad kom til David og gav ham det til Kende, og han sagde til ham: Skal der komme dig syv Aars Hunger i dit Land? eller skal du fly tre Maaneder for din Fjendes Ansigt, og han skal forfølge dig? eller skal der være tre Dage Pest i dit Land? vid nu og se, hvad Svar jeg skal sige den igen, som sendte mig.
Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
14 Og David sagde til Gad: Jeg er saare angest; kære, lad os falde i Herrens Haand, thi hans Barmhjertighed er stor, men jeg vil nødig falde i Menneskens Haand.
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
15 Saa lod Herren Pest komme i Israel fra Morgenen indtil den bestemte Tid, og der døde halvfjerdsindstyve Tusinde Mænd af Folket fra Dan og indtil Beersaba.
Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
16 Og der Engelen udrakte sin Haand over Jerusalem til at ødelægge den, da angrede Herren det onde, og han sagde til Engelen, som ødelagde Folket: Det er nok, drag nu din Haand tilbage; og Herrens Engel var da ved Jebusiteren Aravnas Tærskeplads.
Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
17 Og David sagde til Herren, der han saa Engelen, som slog iblandt Folket, og han sagde: Se, jeg har syndet, og jeg har handlet ilde; men disse Faar, hvad have de gjort? Kære, lad din Haand være imod mig og imod min Faders Hus.
Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
18 Og Gad kom til David paa den samme Dag og sagde til ham: Gak op, oprejs Herren et Alter paa Jebusiteren Aravnas Tærskeplads.
A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
19 Saa gik David op efter Gads Ord, som Herren havde befalet.
Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
20 Og Aravna saa ud og saa Kongen og hans Tjenere komme over til sig; og Aravna gik ud og bøjede sit Ansigt for Kongen til Jorden.
Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
21 Og Aravna sagde: Hvorfor kommer min Herre Kongen til sin Tjener? Og David sagde: For at købe denne Tærskeplads af dig til at bygge Herren et Alter, at denne Plage maa holde op for Folket.
Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
22 Og Aravna sagde til David: Min Herre Kongen tage og ofre det, ham godt synes; se, der er en Okse til Brændofferet og Tærskeslæderne og Tøjet paa Oksen til Veddet.
Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
23 Kong Aravna gav Kongen alt det, og Aravna sagde til Kongen: Herren din Gud have Behagelighed til dig!
Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
24 Men Kongen sagde til Aravna: Ikke saa, men jeg vil købe det af dig for dets Værd, thi jeg vil ikke ofre Brændofre for intet til Herren min Gud. Saa købte David Tærskepladsen og Oksen for halvtredsindstyve Sekel Sølv.
Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
25 Og David byggede Herren der et Alter og ofrede Brændofre og Takofre; og Herren bønhørte Landet, og Plagen holdt op for Israel.
Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.