< 2 Samuel 12 >
1 Og Herren sendte Nathan til David, og der han kom ind til ham, da sagde han til ham: Der var to Mænd i en Stad, en rig og en fattig.
Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Da ya tafi wajensa, sai ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu a wani gari, ɗaya mai arziki, ɗayan kuma matalauci.
2 Den rige havde smaat Kvæg og stort Kvæg, saare meget.
Mai arzikin yana da babban garken tumaki, da kuma shanu,
3 Men den fattige havde aldeles intet uden et lidet Faar, som han havde købt og fødte op, og det var blevet stort hos ham tillige med hans Børn; det aad af hans Brød og drak af hans Bæger og laa i hans Skød, og det var ham som en Datter.
amma matalauci ba shi da kome sai’yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi kiwonta, ta kuwa yi girma tare shi da yaransa. Takan ci tare da shi ta sha ruwa a kwaf nasa, har ma ta kwanta a ƙirjinsa. Ta ma zama kamar’ya a gare shi.
4 Men der en Vandringsmand kom til den rige Mand, da nænnede han ikke at tage af sit smaa Kvæg og af sit store Kvæg for at lave noget til den vejfarende Mand, som kom til ham; men han tog den fattige Mands Faar og lavede det til den Mand, som var kommen til ham.
“To, sai ga wani baƙo ya zo wurin mai arzikin nan, amma mai arzikin ya ƙi yă kama tunkiyarsa, ko saniyarsa yă yanka don yă shirya wa baƙon da ya zo abinci. A maimako, sai ya je ya kama’yar tunkiyan nan ta matalaucin ya yanka ya shirya wa mutumin da ya zo masa.”
5 Da optændtes Davids Vrede saare imod den Mand, og han sagde til Nathan: Saa vist som Herren lever, den Mand er et Dødsens Barn, som det gjorde.
Dawuda ya husata ƙwarai da mutumin, ya ce wa Natan, “Muddin Ubangiji yana a raye, mutumin da ya yi wannan ya cancanci yă mutu!
6 Og han skal betale det Faar firdobbelt, fordi han gjorde denne Gerning, og fordi han ikke viste Skaansel.
Dole yă biya diyyar tunkiyan nan sau huɗu, domin ya aikata haka ba tausayi.”
7 Da sagde Nathan til David: Du er Manden! Saa sagde Herren, Israels Gud: Jeg salvede dig til Konge over Israel, og jeg udfriede dig af Sauls Haand,
Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin! Ga abin da Ubangiji, Allah ya ce, ‘Na naɗa ka sarki bisa Isra’ila, na kuma cece ka daga hannun Shawulu.
8 og jeg gav dig din Herres Hus og din Herres Hustruer i dit Skød og gav dig Israels og Judas Hus, og dersom det var for lidet, da vilde jeg lagt dig saadant og saadant til.
Na ba ka gidan maigidanka, da matan maigidanka duka. Na ba ka gidan Isra’ila da Yahuda. Da a ce dukan waɗannan sun kāsa maka, ai, da na ƙara maka.
9 Hvorfor har du foragtet Herrens Ord, at du gjorde det, som er ondt for hans Øjne? Hethiteren Uria har du slaget med Sværdet, og hans Hustru har du taget dig til Hustru; men ham har du slaget ihjel ved Ammons Børns Sværd.
Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
10 Saa skal nu Sværdet ikke vige fra dit Hus evindeligt, fordi du foragtede mig og tog Hethiteren Urias Hustru, at hun skulde være dig til en Hustru.
To, fa, takobi ba zai taɓa rabu da gidanka ba, domin ka rena ni, ka kuma ƙwace matar Uriya mutumin Hitti ta zama matarka.’
11 Saa sagde Herren: Se, jeg rejser Ulykke over dig fra dit eget Hus og tager dine Hustruer for dine Øjne og giver din Næste dem, at han skal ligge hos dine Hustruer for den klare Sol.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Daga cikin iyalinka zan kawo masifa a kanka. A idanunka zan ɗauki matanka in ba wa wani da yake kusa da kai, zai kuwa kwana da su da rana tsaka.
12 Thi du har gjort det i Løndom; men jeg vil gøre denne Gerning for al Israel og for Solens Lys.
Ka aikata wannan a ɓoye, amma zan aikata wannan da rana tsaka, a gaban dukan Isra’ila.’”
13 Da sagde David til Nathan: Jeg har syndet imod Herren. Og Nathan sagde til David: Herren har ogsaa forladt dig din Synd, du skal ikke dø.
Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce, “Ubangiji ya yafe maka zunubin. Ba za ka mutu ba.
14 Dog, fordi du ved denne Gerning har givet Herrens Fjender Lejlighed til at spotte, skal ogsaa den Søn, som dig er født, visselig dø.
Amma saboda ka yi haka ka sa abokan gāba suka rena Ubangiji, yaron da aka haifa maka zai mutu.”
15 Saa gik Nathan til sit Hus, og Herren slog Barnet, som Urias Hustru havde født David, at det blev sygt.
Bayan Natan ya tafi gida, sai Ubangiji ya bugi yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda, ya kuwa kamu da ciwo.
16 Og David søgte Gud for Drengen, og David fastede meget og gik ind og blev Natten over og laa paa Jorden.
Dawuda ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi, ya kuma shiga gidansa ya kwana kwance a ƙasa.
17 Da opstode de ældste af hans Hus for ham og vilde rejse ham op fra Jorden; men han vilde ikke og aad ikke Brød med dem.
Dattawan iyalinsa suka tsaya kusa da shi don su ɗaga shi daga ƙasa, amma ya ƙi, bai kuwa ci wani abu tare da su ba.
18 Og det skete paa den syvende Dag, da døde Barnet, og Davids Tjenere frygtede for at give ham til Kende, at Barnet var død; thi de sagde: Se, der Barnet var levende, talede vi til ham, og han hørte ikke paa vor Røst, hvorledes skulle vi da sige til ham: Barnet er død? thi det maatte gøre ham ondt.
A rana ta bakwai sai yaron ya rasu. Barorin Dawuda suka ji tsoro su gaya masa cewa yaron ya mutu, gama sun yi tunani cewa, “Yayinda yaron yake da rai, mun yi magana da Dawuda bai ji mu ba. Yaya za mu gaya masa yaron ya mutu? Ai, zai yi wa kansa ɓarna.”
19 Men David saa, at hans Tjenere hviskede, og David forstod, at Barnet var død; og David sagde til sine Tjenere: Er Barnet død? og de sagde: Det er død.
Dawuda ya gane bayinsa suna wa juna raɗan wani abu, sai ya gane yaron ya mutu. Sai ya ce, “Yaron ya rasu ko?” Suka ce, “I, ya rasu.”
20 Da stod David op fra Jorden og toede sig og salvede sig og omskiftede sine Klæder og gik ind i Herrens Hus og bad; og der han kom til sit Hus, da begærede han Mad, og de satte Mad for ham, og han aad.
Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
21 Da sagde hans Tjenere til ham: Hvad er det for en Ting, som du har gjort? du fastede og græd for Barnet, da det levede, men da Barnet er død, staar du op og æder Brød?
Barorinsa suka ce masa, “Me ya sa kake yin haka? Yayinda yaron yake da rai, ka yi azumi, ka kuma yi kuka, amma yanzu da yaron ya mutu, ka tashi, ka kuma ci abinci!”
22 Og han sagde: Der Barnet endnu levede, fastede og græd jeg; thi jeg sagde: Hvo ved? Herren tør vorde mig naadig, at Barnet maa leve.
Ya ce musu, “Yayinda yaron yake da rai, na yi azumi, na kuma yi kuka. Na yi tunani na ce, ‘Wa ya sani? Ko Ubangiji zai yi mini alheri yă bar yaron yă rayu.’
23 Men nu det er død, hvorfor skal jeg da faste? kan jeg endnu hente det tilbage? jeg farer til det, men det kommer ikke tilbage til mig.
Amma yanzu da ya mutu, me zai sa in yi azumi? Zan iya dawo da shi ne? Ni zan je wajensa, ba shi zai dawo wurina ba.”
24 Derefter trøstede David Bathseba sin Hustru og gik ind til hende og laa hos hende, og hun fødte en Søn, og han kaldte hans Navn Salomo, men ham elskede Herren;
Sai Dawuda ya yi wa matarsa Batsheba ta’aziyya, ya kuma tafi wurinta ya kwana da ita. Ta kuma haifi ɗa, suka ba shi suna Solomon. Ubangiji ya ƙaunace shi;
25 og han sendte Bud ved Nathan, Profeten, og denne kaldte hans Navn Jedid-Ja, for Herrens Skyld.
kuma saboda Ubangiji ya ƙaunace shi, sai ya aika da saƙo ta wurin annabi Natan yă ba shi suna Yedidiya.
26 Men Joab stred imod Ammons Børns Rabba og indtog Kongestaden.
Ana cikin haka, sai Yowab ya yi yaƙi da Rabba na Ammonawa, ya kuma ƙwace babban birnin.
27 Og Joab sendte Bud til David og lod sige: Jeg har stridt imod Rabba og har ogsaa indtaget Vandstaden.
Sa’an nan Yowab ya aika manzanni wurin Dawuda yana cewa, “Na yaƙi Rabba na kuma ƙwace hanyar samun ruwanta.
28 Saa saml du nu det øvrige Folk, og belejr Staden, og indtag den, at ikke jeg skal indtage Staden, og jeg skulde blive navnkundig deraf.
Yanzu fa ka tattara saura rundunoni ka fāɗa wa birnin ka ci shi. In ba haka ba zan karɓe birnin, a kuma kira shi da sunana.”
29 Saa samlede David alt Folket og drog til Rabba og stred imod den og indtog den.
Saboda haka Dawuda ya tattara sauran rundunar sojojin suka tafi Rabba suka fāɗa masa suka kuma ci shi.
30 Og han tog deres Konges Krone fra hans Hoved; den havde en Vægt af et Centner Guld og var besat med Ædelstene, og den kom over Davids Hoved, og han udførte af Staden saare meget Bytte.
Ya ɗauke rawanin daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti, na zinariya, an kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, aka aza shi a kan Dawuda. Ya kuma kwashe ganima mai yawa daga garin.
31 Men Folket, som var derudi, førte han ud og lagde dem under Save og Tærskeslæder af Jern og under Økser af Jern og lod dem gaa igennem Teglovnen; og saaledes gjorde han ved alle Ammons Børns Stæder. Siden vendte David og alt Folket tilbage til Jerusalem.
Ya fito da mutanen da suke a can, ya sa su su yi aiki da zarto, da diga, da kuma gatari, ya kuma sa su bugan bulok. Haka ya yi wa dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da dukan sojoji suka koma Urushalima.