< 2 Peter 2 >
1 Men der opstod ogsaa falske Profeter iblandt Folket, ligesom der ogsaa iblandt eder vil komme falske Lærere, som ville liste fordærvelige Vranglærdomme ind, idet de endog fornægte den Herre, som købte dem, og bringe en brat Undergang over sig selv,
Amma a dā akwai annabawan ƙarya a cikin mutane, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku. A ɓoye za su shigar da karkataccen koyarwa mai hallaka, har ma su yi mūsun Ubangiji mai iko duka wanda ya saye su suna kawo wa kansu hallaka farat ɗaya.
2 og mange ville efterfølge deres Uterligheder, saa Sandhedens Vej for deres Skyld vil blive bespottet,
Da yawa za su bi hanyoyinsu na rashin kunya su kuma sa a rena hanyar gaskiya.
3 og i Havesyge ville de med falske Ord skaffe sig Vinding af eder; men Dommen over dem har alt fra gamle Dage været i Virksomhed, og deres Undergang slumrer ikke.
Cikin kwaɗayinsu waɗannan malaman ƙarya za su cuce ku da tatsuniyoyin da suka ƙaga. Hukuncinsu yana a rataye a kansu tun da daɗewa, hallakarsu kuma ba ta barci.
4 Thi naar Gud ikke sparede Engle, da de syndede, men nedstyrtede dem i Afgrunden og overgav dem til Mørkets Huler for at bevogtes til Dom, (Tartaroō )
Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō )
5 og ikke sparede den gamle Verden, men bevarede Retfærdighedens Prædiker Noa selv ottende, da han førte Oversvømmelse over en Verden af ugudelige
in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;
6 og lagde Sodomas og Gomorras Stæder i Aske og domfældte dem til Ødelæggelse, saa han har sat dem til Forbillede for dem, som i Fremtiden vilde leve ugudeligt,
in har ya hukunta biranen Sodom da Gomorra ta wurin ƙone su suka zama toka, ya kuma maishe su misali na abin da zai faru da marasa tsoron Allah;
7 og udfriede den retfærdige Lot, som plagedes af de ryggesløses uterlige Vandel,
in kuwa har ya ceci Lot, mai adalci, wanda ya damu ainun da ƙazamar rayuwar mutane marasa bin doka;
8 (thi medens den retfærdige boede iblandt dem, pintes han Dag for Dag i sin retfærdige Sjæl ved de lovløse Gerninger, som han saa og hørte):
(adon kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa’ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci)
9 — Da ved Herren at udfri gudfrygtige af Fristelse, men at straffe og bevogte uretfærdige til Dommens Dag,
in haka ne, to, Ubangiji ya san yadda zai ceci mutane masu tsoron Allah daga gwaje-gwaje, yă kuma tsare marasa adalci don ranar hukunci, har yă zuwa ranar shari’a.
10 og mest dem, som vandre efter Kød, i Begær efter Besmittelse, og foragte Herskab. Frække, selvbehagelige, bæve de ikke ved at bespotte Herligheder,
Wannan gaskiya ce musamman ga waɗanda suke bin sha’awace-sha’awacen lalaci na mutuntaka, suna kuma rena masu mulki. Da ƙarfin hali da kuma girman kai, waɗannan mutane ba sa tsoro kawo zargin ɓata sunan talikan sama;
11 hvor dog Engle, som ere større i Styrke og Magt, ikke fremføre bespottende Dom imod dem for Herren.
duk da haka ko mala’iku ma da suka fi su ƙarfi suka kuma fi su iko, ba sa kawo irin wannan zargi na ɓata suna game da waɗannan talikai a gaban Ubangiji.
12 Men disse — ligesom ufornuftige Dyr, der af Natur ere fødte til at fanges og ødelægges, skulle de, fordi de bespotte, hvad de ikke kende, ogsaa ødelægges med hines Ødelæggelse,
Amma waɗannan mutane suna yin saɓo a kan abubuwan da ba su fahimta ba. Suna kama da dabbobi marasa hankali, halittun da suke bin abin da jikinsu ya faɗa musu kawai, waɗanda aka haifa don a kama a hallaka, kuma kamar dabbobi su ma za su hallaka.
13 idet de faa Uretfærdigheds Løn. De sætte deres Lyst i Vellevned om Dagen, disse Skampletter og Skændselsmennesker! De svælge i deres Bedragerier, medens de holde Gilde med eder;
Za a yi musu sakamako da muguntar da suka yi. A ra’ayinsu jin daɗi shi ne a yi annashuwa da rana tsaka. Su ƙazamai ne marasa kunya, suna cike da jin daɗin sha’awace-sha’awacensu yayinda suke cin biki tare da ku.
14 deres Øjne ere fulde af Horeri og kunne ikke faa nok af Synd; de lokke ubefæstede Sjæle; de have et Hjerte, øvet i Havesyge, Forbandelsens Børn;
Idanunsu sun cike da zina, ba sa ƙoshi da yin zunubi; suna jarrabtar waɗanda ba tsayayyu ba; gwanaye ne a kan kwaɗayi, la’anannun iri!
15 de have forladt den lige Vej og ere farne vild, følgende Bileams, Beors Søns, Vej, han, som elskede Uretfærdigheds Løn,
Sun bar miƙaƙƙiyar hanya suka bauɗe suna bin hanyar Bala’am ɗan Beyor, wanda ya yi ƙaunar hakkin mugunta.
16 men fik Revselse for sin Overtrædelse: Et umælende Trældyr talte med menneskelig Røst og hindrede Profetens Afsind.
Amma an tsawata masa saboda laifinsa ta wurin jaki, dabbar da ba ta magana, wadda ta yi magana da muryar mutum ta kuma kwaɓi haukan annabin.
17 Disse ere vandløse Kilder og Taageskyer, som drives af Stormvind; for dem er Mørke og Mulm bevaret.
Waɗannan mutane maɓulɓulai ne babu ruwa da kuma hazon da guguwar iska take kora. An shirya matsanancin duhu dominsu.
18 Thi dem, som ere lige ved at undslippe fra dem, der vandre i Vildfarelse, lokke de i Kødets Begæringer ved Uterligheder, idet de tale Tomheds overmodige Ord
Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
19 og love dem Frihed, skønt de selv ere Fordærvelsens Trælle; thi man er Træl af det, som man er overvunden af.
Suna yin musu alkawarin’yanci, yayinda su kansu bayi ne ga aikin lalata gama mutum bawa ne ga duk abin da ya mallake shi.
20 Thi dersom de, efter at have undflyet Verdens Besmittelser ved Erkendelse af vor Herre og Frelser Jesus Kristus, igen lade sig indvikle deri og overvindes, da er det sidste blevet værre med dem end det første.
In har sun kuɓuta daga lalacin duniya ta wurin sanin Ubangijinmu da kuma Mai Cetonmu Yesu Kiristi sai suka sāke koma a cikin lalacin, har ya rinjaye su, za su fi muni a ƙarshe fiye da farko.
21 Thi bedre havde det været dem ikke at have erkendt Retfærdighedens Vej end efter at have erkendt den at vende sig bort fra det hellige Bud, som var blevet dem overgivet.
Zai fi musu kyau da ba su taɓa sanin hanyar adalci ba, fiye da a ce sun sani sa’an nan su juya bayansu ga umarni mai tsarkin nan da aka ba su.
22 Det er gaaet dem efter det sande Ordsprog: „Hunden vender sig om til sit eget Spy, og den toede So til at vælte sig i Sølen.”
A kansu karin maganan nan gaskiya ce, “Kare ya koma kan amansa,” da kuma, “Alade da aka yi wa wanka, ya koma birgimarsa cikin laka.”