< 2 Peter 1 >
1 Simon Peter, Jesu Kristi Tjener og Apostel, til dem, der have faaet samme dyrebare Tro som vi ved vor Guds og Frelsers Jesu Kristi Retfærdighed:
Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.
2 Naade og Fred vorde eder mangfoldig til Del i Erkendelse af Gud og vor Herre Jesus.
Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.
3 Saasom hans guddommelige Magt har skænket os alt, hvad der hører til Liv og Gudfrygtighed ved Erkendelsen af ham, som kaldte os ved sin Herlighed og Kraft,
Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa.
4 hvorved han har skænket os de største og dyrebare Forjættelser, for at I ved disse skulle faa Del i guddommelig Natur, naar I undfly Fordærvelsen i Verden, som har sin Grund i Begær,
Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.
5 saa anvender just derfor al Flid paa i eders Tro at udvise Dyd og i Dyden Kundskab
Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani;
6 og i Kundskaben Afholdenhed og i Afholdenheden Udholdenhed og i Udholdenheden Gudsfrygt
ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah;
7 og i Gudsfrygten Broderkærlighed og i Broderkærligheden Kærlighed.
ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga’yan’uwa; ga nuna alheri ga’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna.
8 Thi naar dette findes hos eder og er i Tiltagen, lader det eder ikke staa ørkesløse eller ufrugtbare i Erkendelsen af vor Herre Jesus Kristus;
Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 den nemlig, som ikke har dette, er blind, svagsynet, idet han har glemt Renselsen fra sine fordums Synder.
Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.
10 Derfor, Brødre! gører eder des mere Flid for at befæste eders Kaldelse og Udvælgelse; thi naar I gøre dette, skulle I ingen Sinde støde an.
Saboda haka’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba,
11 Thi saa skal der rigelig gives eder Indgang i vor Herres og Frelsers Jesu Kristi evige Rige. (aiōnios )
za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios )
12 Derfor vil jeg ikke forsømme altid at paaminde eder om dette, ihvorvel I vide det og ere befæstede i den Sandhed, som er til Stede hos os.
Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu.
13 Men jeg anser det for ret at vække eder ved Paamindelse, saa længe jeg er i dette Telt,
A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki,
14 da jeg ved, at Aflæggelsen af mit Telt kommer brat, saaledes som jo vor Herre Jesus Kristus har givet mig til Kende.
domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari.
15 Og jeg vil ogsaa gøre mig Flid for, at I til enhver Tid efter min Bortgang kunne drage eder dette i Minde.
Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.
16 Thi vi have ikke fulgt kløgtigt opdigtede Fabler, da vi kundgjorde eder vor Herres Jesu Kristi Kraft og Tilkommelse, men vi have været Øjenvidner til hans Majestæt,
Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido.
17 nemlig da han fik Ære og Herlighed af Gud Fader, idet en saadan Røst lød til ham fra den majestætiske Herlighed: „Denne er min Søn, den elskede, i hvem jeg har Velbehag.”
Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
18 Og vi hørte denne Røst lyde fra Himmelen, da vi vare med ham paa det hellige Bjerg.
Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.
19 Og des mere stadfæstet have vi det profetiske Ord, hvilket I gøre vel i at agte paa som paa et Lys, der skinner paa et mørkt Sted, indtil Dagen bryder frem, og Morgenstjernen oprinder i eders Hjerter,
Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku.
20 idet I fornemmelig mærke eder dette, at ingen Profeti i Skriften beror paa egen Tydning.
Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa.
21 Thi aldrig er nogen Profeti bleven fremført ved et Menneskes Villie; men drevne af den Helligaand talte hellige Guds Mænd.
Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.