< Anden Kongebog 7 >
1 Da sagde Elisa: Hører Herrens Ord! saa sagde Herren: I Morgen ved denne Tid skal en Maade Mel koste en Sekel, og to Maader Byg en Sekel i Samarias Port.
Sai Elisha ya ce, “Ku ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji ya ce, gobe war haka, za a sayar da mudun gari mai laushi a farashin shekel guda, mudu biyu na sha’ir kuma a shekel ɗaya a ƙofar birnin Samariya.”
2 Men Høvedsmanden, til hvis Haand Kongen hældede sig, svarede den Guds Mand og sagde: Se, om Herren gjorde Vinduer paa Himmelen, mon dette Ord kunde ske? og han sagde: Se, du skal se det med dine Øjne, men ikke æde deraf.
Sai wani hafsa mataimakin sarki ya ce wa mutumin Allah, “Kai, ko da Ubangiji zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba!” Sai Elisha ya ce, “Za ka gani da idanunka, zai faru, amma ba za ka ci ba!”
3 Men der var fire spedalske Mænd, ved Indgangen til Porten, og de sagde den ene til den anden: Hvorfor blive vi her, indtil vi dø?
To, akwai waɗansu kutare huɗu a ƙofar gari. Suka ce wa junansu, “Don me za mu zauna a nan sai mun mutu?
4 Om vi sige: Vi ville gaa ind i Staden, saa er der Hunger i Staden, og vi dø der, og om vi blive her, da maa vi og dø; saa kommer nu og lader os gaa over til Syrernes Lejr, lade de os leve, saa leve vi, og dræbe de os, saa dø vi.
In muka ce, ‘Za mu shiga cikin birni’ yunwa tana can, za mu kuwa mutu. Idan kuwa muka zauna a nan, za mu mutu. Saboda haka, bari mu ƙetare zuwa sansanin Arameyawa mu miƙa kai. Idan suka bar mu da rai, to; idan kuwa suka kashe mu, shi ke nan.”
5 Og de gjorde sig rede i Tusmørket at komme til Syrernes Lejr; der de kom til det yderste af Syrernes Lejr, se, da var der ikke en Mand.
Da yamma sai suka tashi suka tafi sansanin Arameyawa. Yayinda suka shiga tsakiyar sansanin Arameyawa kuwa, sai suka tarar ba kowa a can,
6 Thi Herren havde ladet Syrernes Lejr høre en Lyd af Vogne og en Lyd af Heste, ja, en Lyd af en stor Hær, og de sagde, den ene til den anden: Se, Israels Konge har lejet imod os Hethiternes Konger og Ægypternes Konger til at komme over os.
gama Ubangiji ya sa rundunar Arameyawa suka ji motsin kekunan yaƙi, da motsin dawakai, da na babban rundunar sojoji, saboda haka suka ce wa juna; “Duba, sarkin Isra’ila ya ɗauka hayar sarakuna Hittiyawa da sarakunan Masarawa don su yaƙe mu!”
7 Derfor gjorde de sig rede og flyede i Tusmørket og forlode deres Telte og deres Heste og deres Asener og Lejren, som den stod, og flyede for at redde deres Liv.
Saboda haka suka tashi, suka gudu da yamma, suka bar tentunansu, da dawakansu, da jakunansu. Suka bar sansanin yadda yake, suka gudu don su ceci rayukansu.
8 Der disse spedalske kom til det yderste af Lejren, da kom de til et Telt og aade og drak og toge derfra Sølv og Guld og Klæder og gik bort og skjulte det, og de vendte tilbage og kom til et andet Telt og toge ogsaa noget derfra og gik bort og skjulte det.
Da kutaren nan suka kai bakin sansanin, sai suka shiga wani tenti, suka ci, suka sha, suka kwashi azurfa, da zinariya, da riguna, suka tafi, suka ɓoye su. Sa’an nan suka koma, suka shiga wani tenti, sai suka kwashi kaya daga ciki, suka kuma ɓoye su.
9 Da sagde de, den ene til den anden: Vi gøre ikke ret, denne Dag er et godt Budskabs Dag, og skulde vi tie? dersom vi bie, indtil det bliver lys Morgen, da rammer vor Misgerning os; velan da, lader os gaa og give det til Kende for Kongens Hus!
Sa’an nan suka ce wa juna, “Ba mu yi abin kirki ba. Wannan rana ce ta albishiri amma muka yi shiru; in kuwa mun bari har gari ya waye, to, fa, wata masifa za tă fāɗo mana. Bari mu tafi nan take mu faɗa a fadan sarki.”
10 Og der de kom, raabte de til Stadens Portvagt, og de gave den det til Kende og sagde: Vi kom til Syrernes Lejr, og se, der var ikke en Mand eller et Menneskes Røst, men Heste bundne og Asener bundne og Teltene, saaledes som de vare.
Saboda haka suka je suka kira masu tsaron ƙofar birni, suka ce musu, “Mun je sansanin Arameyawa, ga shi kuwa ba mu iske kowa a can ba, babu ko motsin wani, sai dai dawakai da jakuna a daure, tentunan kuwa suna nan yadda suke.”
11 Da raabte Portvagten og forkyndte det inde i Kongens Hus!
Sai matsaran ƙofar suka sanar da labarin a cikin fada.
12 Og Kongen stod op om Natten og sagde til sine Tjenere: Jeg vil kundgøre eder, hvad Syrerne have gjort imod os: De vide, at vi lide Hunger, derfor ere de udgangne af Lejren for at skjule sig paa Marken, sigende: Naar de gaa ud af Staden, da ville vi gribe dem levende og komme ind i Staden.
Sai sarki ya tashi da daren nan ya ce wa hafsoshinsa, “Na san abin da Arameyawan suke shiri! Sun san game da yunwar da muke ciki a nan, domin haka sun bar sansaninsu suka shiga jeji suka ɓuya, suna nufin sa’ad da muka fita daga birni, sai su kama mu da rai, sa’an nan su shiga birnin.”
13 Da svarede en af hans Tjenere og sagde: Lad dem dog tage fem af Hestene, som ere tilovers, som ere overblevne herinde; se, de ere som al Israels Hob, som ere overblevne herinde, se, de ere som al Israels Hob, der er omkommen; og lader os dog sende hen og se til!
Ɗaya daga cikin fadawan sarki ya ce, “A sa waɗansu mutane su ɗauki dawakai biyar da suka ragu cikin birni, idan ba su tsira ba, za su zama kamar sauran Isra’ilawan da suka riga suka mutu ne. Bari mu aika, mu gani.”
14 Da toge de to Vogne med Heste, og Kongen sendte dem efter Syrernes Hær og sagde: Drager hen og ser til!
Saboda haka suka zaɓi kekunan yaƙi biyu tare da dawakansu, sarki kuwa ya aike su su bi bayan sojojin Arameyawa. Ya umarci masu tuƙinsu ya ce, “Ku je ku bincika abin da ya faru.”
15 Og der de droge efter dem indtil Jordanen, se, da laa hele Vejen fuld af Klæder og Tøj, som Syrerne havde kastet fra sig, der de hastede af Sted; og Budene kom igen og gave Kongen det til Kende.
Suka bi sawunsu har Urdun, suka ga tufafi da makamai barjat ko’ina a hanya waɗanda Arameyawa suka zubar yayinda suke gudu. Sai’yan aika suka dawo suka ba wa sarki labari.
16 Saa gik Folket ud og plyndrede Syrernes Lejr; og en Maade Mel kostede en Sekel og to Maader Byg en Sekel, efter Herrens Ord.
Sa’an nan jama’a suka fita suka kwashi ganima a sansanin Arameyawa. Aka kuwa sayar da gari mai laushi a farashin shekel guda, mudu biyu na sha’ir kuma a shekel guda, yadda Ubangiji ya faɗi.
17 Men Kongen beskikkede den Høvedsmand, hvis Haand han hældede sig til, til at være ved Porten, og Folket traadte ham ned i Porten, saa at han døde, ligesom den Guds Mand havde talt, som havde talt det, der Kongen kom ned til ham.
Sai ya kasance cewa Sarki ya sa dogari wanda ya raka shi wajen Elisha ya tsare ƙofar birnin. Sai mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu, kamar yadda annabi Elisha ya faɗa sa’ad da sarki ya tafi wurinsa.
18 Thi det skete, som den Guds Mand havde talt til Kongen og sagt: I Morgen paa denne Tid skulle to Maader Byg koste en Sekel og en Maade Mel en Sekel i Samarias Port.
Haka kuwa ya kasance kamar yadda mutumin Allah ya ce wa sarki, “Gobe war haka, za a sayar da mudun gari shekel guda, mudun sha’ir biyu ma a shekel guda, a ƙofar Samariya.”
19 Og Høvedsmanden havde svaret den Guds Mand og sagt: Ja se, om Herren gjorde Vinduer paa Himmelen, mon det kunde ske efter dette Ord? og han havde sagt: Se, du skal se det med dine Øjne og ikke æde deraf.
Hafsan ya riga ya ce wa mutumin Allah, “Kai, ko da Ubangiji zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba!” Mutumin Allah kuwa ya faɗa masa, “Za ka gani da idanunka sai dai ba za ka ci ba!”
20 Og det gik ham saaledes; thi Folket traadte ham ned i Porten, saa at han døde.
Haka kuwa ya kasance, gama mutane sun tattake shi a hanyar shiga, har ya mutu.