< Anden Kongebog 15 >
1 Idet syv og tyvende Jeroboams, Israels Konges, Aar blev Asaria, Amazias, Judas Konges, Søn, Konge.
A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Han var seksten Aar gammel, der han blev Konge, og regerede to og halvtredsindstyve Aar i Jerusalem, og hans Moders Navn var Jekolia fra Jerusalem.
Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
3 Og han gjorde det, som var ret for Herrens Øjne, efter alt det, som hans Fader Amazia gjorde.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
4 Dog kom Højene ikke bort; Folket ofrede endnu og gjorde Ragelse paa Højene.
Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
5 Og Herren slog Kongen, at han blev spedalsk indtil sin Dødsdag og boede udi et særskilt Hus; men Jotham, Kongens Søn, var over Huset og dømte Folket i Landet.
Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
6 Men det øvrige af Asarias Handeler og alt, hvad han gjorde, er det ikke skrevet i Judas Kongers Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
7 Og Asaria laa med sine Fædre, og de begavede ham hos hans Fædre i Davids Stad, og Jotham, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
8 Og i det otte og tredivte Asarias, Judas Konges, Aar blev Sakaria, Jeroboams Søn, Konge over Israel i Samaria seks Maaneder.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
9 Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, ligesom hans Fædre gjorde, han veg ikke fra Jeroboams, Nebats Søns, Synder, som han kom Israel til at synde med.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
10 Og Sallum, Jabes's Søn, gjorde et Forbund imod ham og slog ham i Folkets Paasyn og dræbte ham og blev Konge i hans Sted.
Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
11 Men det øvrige af Sakarias Handeler, se, de Ting ere skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog.
Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
12 Dette er Herrens Ord, som han talte til Jehu, sigende: Dine Sønner i det fjerde Led skulle sidde paa Israels Trone; og det skete saa.
Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
13 Sallum, Jabes's Søn, blev Konge i det ni og tredivte Usias, Judas Konges, Aar, og regerede en Maaneds Tid i Samaria.
Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
14 Og Menahem, Gadis Søn, drog op fra Thirza og kom til Samaria og slog Sallum, Jabes's Søn, i Samaria og dræbte ham og blev Konge i hans Sted.
Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
15 Men det øvrige af Sallums Handeler og hans Forbund, som han indgik, se, de Ting ere skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog.
Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 Da slog Menahem Thipsa og alle, som vare deri, og dens Landemærke, da han drog ud fra Thirza; fordi man ikke havde villet indlade ham, derfor slog han dem; alle de frugtsommelige derudi søndersled han.
A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
17 Og i det ni og tredivte Asarias, Judas Konges, Aar blev Menahem, Gadis Søn, Konge over Israel, ti Aar i Samaria.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
18 Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, han veg ikke fra Jeroboams, Nebats Søns, Synder, som han kom Israel til at synde med, alle sine Dage.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
19 Ful, Kongen af Assyrien, kom over Landet, og Menahem gav Ful tusinde Centner Sølv, at han skulde holde med ham og befæste Riget i hans Haand.
Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
20 Og Menahem indkrævede det Sølv af Israel, af alle de formuende, til at give Kongen af Assyrien, nemlig halvtredsindstyve Sekel Sølv for hver Mand; saa drog Kongen af Assyrien tilbage og blev ikke der i Landet.
Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
21 Men det øvrige af Menahems Handeler og alt det, han gjorde, er det ikke skrevet i Israels Kongers Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
22 Og Menahem laa med sine Fædre, og Pekaja, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
23 I det halvtredsindstyvende Asarias, Judas Konges, Aar blev Pekaja, Menahems Søn, Konge over Israel i Samaria i to Aar.
A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
24 Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, han veg ikke fra Jeroboams, Nebats Søns, Synder, som han kom Israel til at synde med.
Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
25 Og Peka, Remalias Søn, hans Høvedsmand, gjorde et Forbund imod ham og ihjelslog i Samaria, i Kongens Hus's Palads, ham og Argob og Arje; og han havde med sig halvtredsindstyve Mænd af Gileaditernes Børn og dræbte ham og blev Konge i hans Sted.
Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
26 Men det øvrige af Pekajas Handeler og alt det, han gjorde, se, de Ting ere skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog.
Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
27 I det to og halvtredsindstyvende Asarias, Judas Konges, Aar blev Peka, Remalias Søn, Konge over Israel i Samaria i tyve Aar.
A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
28 Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne, han veg ikke fra Jeroboams, Nebats Søns, Synder, som han kom Israel til at synde med.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
29 I Pekas, Israels Konges, Dage kom Thiglath-Pileser, Kongen af Assyrien, og tog Ijon og Abel-Beth-Maaka og Ianoa og Kedes og Hasor og Gilead og Galilæa, alt Nafthalis Land, og han bortførte dem til Assyrien.
A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
30 Og Hosea, Elas Søn, gjorde et Forbund imod Peka, Remalias Søn, og slog ham og dræbte ham og blev Konge i hans Sted, i det tyvende Jothams, Ussias Søns, Aar.
Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
31 Men det øvrige af Pekas Handeler og alt det, han gjorde, se, de Ting ere skrevne i Israels Kongers Krønikers Bog.
Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 I det andet Pekas, Remalias Søns, Israels Konges, Aar blev Jotham, en Søn af Judas Konge Ussia, Konge.
A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
33 Han var fem og tyve Aar gammel, der han blev Konge, og han regerede seksten Aar i Jerusalem, og hans Moders Navn var Jerusa, Zadoks Datter.
Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
34 Og han gjorde det, som var ret for Herrens Øjne, efter alt det, som Ussia, hans Fader, gjorde.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
35 Dog blev Højene ikke borttagne, Folket ofrede endnu og gjorde Røgelse paa Højene; han byggede den øverste Port paa Herrens Hus.
Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
36 Men det øvrige af Jothams Handeler og alt det, han gjorde, ere de Ting ikke skrevne i Judas Kongers Krønikers Bog?
Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
37 I de Dage begyndte Herren at sende Rezin, Kongen af Syrien, og Peka, Remalias Søn, mod Juda.
(A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
38 Og Jotham laa med sine Fædre og blev begraven hos sine Fædre i Davids, sin Faders, Stad, og Akas, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.